Connect with us

Ƙasashen Ƙetare

Buhari zai tafi kasar Liberia domin taya su murnar cika shekaru 175 da samun ‘yancin kai

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, zai bar Najeriya zuwa kasar Laberiya, domin halartar bikin murnar cika shekaru 175 da samun ‘yancin kai, a matsayin kasa mafi tsufa a Afirka bayan samun ‘yancin kai.

Babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai, da wayar da kan jama’a, Garba Shehu, a wata sanarwa da ya fitar jiya, ya ce, shugaba Buhari zai bar Najeriya a yau Talata, inda zai gabatar da jawabi, inda ya kara da cewa, tafiyar na nuni da muhimmancin da aka baiwa tsaro da walwalar Laberiya da sauran kasashen yammacin Afirka.

“Ana sa ran shugaban kasa ya jaddada muhimmancin mutunta tsarin doka a fadin yankin. Idan babu tsarin doka da tsarin mulki, ba za a iya samun zaman lafiya da ci gaba ba.

“Tafiya zuwa Laberiya ta zo ne a daidai lokacin da rashin kwanciyar hankali na siyasa da kuma dawo da juyin mulkin da aka yi ya inganta tsarin dimokuradiyya na shekaru biyu zuwa talatin a yankin.

“Laberiya da Saliyo tare da Najeriya za su yi zabe a 2023, kuma ana sa ran sShugaba Buhari zai jaddada musu mahimmancin zabe mai inganci da inganci.” In ji Garba Shehu.

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji Sun yi juyin Mulki a Gabon

Published

on

Sojoji sun bayyana a gidan talabijin na kasar Gabon tare da sanar da karbi mulki.

Sun ce sun soke sakamakon zaben da ka gudanar ranar Asabar, inda aka ayyana shugaba Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukumar zaben ta ce Mr Bongo ya samu nasara ne da kasa da kashi biyu bisa uku na kuri’un da aka kada a zaben da ‘yan adawa suka ce an tafka magudi.

Sun Kuma ce Hambarar da shi zai kawo karshen mulkin shekaru 53 da iyalan gidansu ke yi a Gabon.

Sojoji 12 ne suka bayyana a gidan talabijin dake sanar da soke sakamakon zaben tare da rusa dukkan hukumomin kasar.

Daya daga cikin sojojin ya fada a tashar talabijin ta Gabon 24 cewa, “Mun yanke shawarar kare zaman lafiya ta hanyar kawo karshen mulkin da ake yi a yanzu.”

Mr Bongo ya hau karagar mulki lokacin da mahaifinsa Omar ya rasu a shekara ta 2009.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji sunyi juyin Mulki a jamhuriyar Nijar

Published

on

Rahotanni daga jamhuriyar Nijar na cewa Sojojin Kasar sun yi juyin Mulki, tare da sanar da kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum.

Cikin sanarwar da suka bayar a gidan telebijin din Kasar, jagoran tawagar sojojin Kanal Amadu Abdramane yace “mun kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum tare da karbe dukkanin Wani Iko”.

Sojojin dai sun bayar da dalilin halin rashin tabbas da Kuma Matsin tattalin arziki a kasar.

Tuni dai sojojin suka garkame dukkanin iyakokin Kasar tare da Sanya dokar takaita zirga zirga daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Tun a safiyar laraba ne dai aka wayi gari da fara wancan yunkuri, Wanda yanzu haka ta tabbata, Kasar Nijar na hannun sojoji, Wanda shi ne Karo na hudu ana gudanar da juyin mulkin a jamhuriyar Nijar.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

An tsaurara tsaro a fadar shugaban Kasar Nijar

Published

on

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar, na nuni da cewa dakarun da ke gadin fadar shugaban ƙasa sun rufe duk wata hanyar shiga fadar a wani lamari da ba a kai ga ganowa ba.

Sai dai rahotanni na cewa yanzu haka wasu daga cikin tsofaffin shugabannin ƙasar ta Nijar na tattaunawa da sojojin domin sasanta lamarin.

Karin bayani nan tafe….

Continue Reading

Trending