Connect with us

Labarai

Tsaro: KAROTA ta kama matasan da suke kwana a karkashin gadar sama a Kano

Published

on

Hukumar kula da Zirga-zirga Ababen Hawa ta jiha KAROTA, ta cafke wasu matasa waɗanda ake zargin ɓata-gari ne.

Jami’an sintiri na hukumar ta KAROTA ne suka sami nasarar cafke matasan da daddare a ƙarƙashin shatale-talen Gadar Dangi da ke cikin birnin Kano.

Ɗaya daga cikin jami’an mai suna Mas’ud Ya’u Yusuf, ya bayyana wa hukumar ta KAROTA yadda suka sami nasarar cafke ɓata-garin a lokacin da suka iske su suna kwance a ƙarƙashin gadar, inda suka same su da nau’ikan kayan shaye-shaye da makamai a tare da su.

Sun bayyana musu cewa, yau kwanansu huɗu da shigowa garin Kano. A cewar jami’in hulda da jama’a, Nabulisi Abubakar Kofar Na’isa.

A binciken da hukumar ta gudanar ta gano matasan sun shigo jihar Kano ne daga jihohin Katsina da Zamfara.

Mas’ud Ya’u ya ƙara da cewa, lokacin da suke tsaka da binciken matasan sai wasu ‘yan ƙungiyar Yansintire ta wannan unguwa suka buƙaci a damƙa musu waɗannan ɓata-gari, domin ƙara fadada bincike, saboda sun shaidawa jami’an na KAROTA cewa, ana yi musu ɗauke-ɗauke a cikin unguwar.

Yan sintirin sun bayyana cewa, kwanakin baya sun sami nasarar cafke wasu ɓata-garin waɗanda suke satar kayan Gwamnati da kuma shiga gidajen al’umma domin yi musu sata.

Bayan kammala binke Hukumar ta KAROTA ta miƙa su a hannun jami’an Yansanda na ‘Yar Akwa domin faɗaɗa bincike tare da ɗaukar mataki na gaba.

Shugaban Hukumar KAROTA Hon. Baffa Babba Ɗan’agundi ya yaba wa ƙoƙarin jami’an, sannan ya yi kira ga ɗaukacin al’umma da su cigaba da kai rahoton duk wani motsi na waɗansu mutane waɗanda basu yarda da su ba domin tabbatar da tsaron unguwanni da ma jiha baki ɗaya.

Labarai

Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.

Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.

Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.

Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.

A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Continue Reading

Labarai

Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.

Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.

“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.

Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.

Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Continue Reading

Labarai

Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Published

on

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.

Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.

Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.

Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

Continue Reading

Trending