Connect with us

Manyan Labarai

Zan goyi bayan yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulki saboda ƴan ƙasa – Atiku

Published

on

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi alkawarin cewa, zai goyi bayan kwaskwarima ga kundin tsarin mulki, domin daukaka darajar ƴan kasa idan ya samu dama a zaɓen 2023.

A cikin sanarwar da mai taimaka masa a kan harkokin yaɗa labarai, Abdulrasheed Shehu, ya sanya wa hannu tare da aike wa Dala FM, ya rawaito cewa, Atiku na wannan kalan ne a wani taro da matasan Jam’iyyar PDP a fadin ƙasa, su ka kaddamar da wani shiri mai taken PDP sabon karni, a dakin taro na Shehu Musa Yar’adua dake Abuja, domin wayar da kan yan Najeriya.

A cikin mahalarta taron harda shi kan sa dan takarar shugabancin kasa, Atiku Abubakar da mataimakin sa Sanata Ifeanyi Okowa, sai shugaban Jam’iyyar, Sanata Dr Iyorchia Ayu da Boni Haruna da Liyel Imoke, tsohon gwamnan Cross River da gwamnan jihar Taraba gami da tsofaffin sanatoci da yan majalisar wakilai masu ci da kuma sauran jiga-jigan Jam’iyyar PDP.

A jawabin sa, dan takarar shugaban kasar, ya godewa matasan bisa wannan yunkuri, inda ya bukaci da su zage dantse, domin gina cigaba da hadin kan kasa. Ya jaddada bukatar samun gwamnati wadda za ta tallafawa matasa da mata, domin basu damar aiki da basirar su ga aikin gina kasa.

Sanarwar ta kuma ce, kamar yadda ya fada a yayin gangamin yakin neman zaben gwamnan jihar Osun, ya bukaci matasan su karbi katunan zaben su, kuma su shirya yin zabe tare da kare kuri’ansu.

A nasa bangaren, shugaban Jam’iyyar PDP na kasa, ya godewa matasan, bisa bujuro da wannan tsari, inda ya yi kira a garesu su yi aiki tare da Wazirin Adamawa wanda ya ce, ya sanya dukiyar sa ta kashin Kai a ilimantar da matasa a dukkan matakai, kuma yana cikin wadanda suka tsara managartan manufofi kan ilimi a can baya.

Babban mai jawabi a yayin taron, Emana Ambrose Amawhe Wanda Yar’ Takarar mataimakin gwamna ce a zaben badi, ta godewa tsohon mataimakin shugaban kasar kasancewar sa Mai farfado da kyakkyawan fata ga mutane, inda tace suna tare da Atiku Abubakar, saboda kyakkyawan kundin manufofin sa da kuma son sa ga tafiya tare da kowa domin zaman lafiya da fahimtar juna.

Wadanda suka shirya taron sun ce, sun kaddamar da kashin farko na tsarin a ranar 24 ga watan Afrilun bana, Inda suka ce wannan shi ne na biyu, kuma taken sa shi ne sake tsara Najeriya Wanda ke nufin sake hade kan jama’a, habaka tattalin arziki da ilimi da ingantaccen tsarin fedaraliyya . Kuma sun yi alkawarin wayar da kai da horar da yan Najeriya domin su fahimci nauyin dake kan su a matsayin su na yan kasa.

Manyan Labarai

Wata Sabuwa: Lauya ya nemi kotu ta kama kwamishinan Shari’a na jihar Kano

Published

on

Wani lauya mai zaman kan sa a jihar Kano Barista Haruna Musa Muhammad, ya yi ƙorafi a gaban babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar, akan ta kama kwamishinan Shari’a na jihar Kano Barista Haruna Isah Dederi, da wasu manyan mukarraban gwamnatin jihar.

Lauyan wanda yake wakiltar mai kara Nura Bashir Ahmad, ya bayyana cewar gwamnatin jihar Kano ta rushe wa Nura gida duk da cewar ya samu hukunci a babbar kotun tarayya akan kada a rushe masa gidan.

Cikin wata ƙunshin Shari’a mai lamba FHC/KN/CS/240/2023, mai Shari’a Simon Amobida, ya ayyana cewar kotun tarayya ta gamsu da takardun mallaka da mai ƙara Bashir Ahmad ya gabatar mata, don haka ne ma ta ayyana cewar gidan mallakinsa ne.

Kotun dai tun a ranar 13 ga watan biyu na shekarar da ta gabata ta 2024, ta zartas da hukuncin akan batun.

Mai karar Bashir ta bakin lauyansa Barista Haruna Musa, sun bayyana cewar sun rubuta koke zuwa gaban kotun da ta yi hukuncin tun da dai suna zargin waɗanda ake ƙarar sun raina wannan hukunci kamar yadda ya bayyana a zantawar sa da wakilin Dala FM Kano.

Akan wannan batu ne wakilin namu ya tuntuɓi kwamishinan Shari’a na jihar Kano Barista Haruna Isah Dederi, ta wayar salula, sai dai bai samu damar ɗaa wayar ba, ya kuma aike masa da gajeren saƙon kar ta kwana nan ma bai bada amsa ba, amma yana dakon sa.



Continue Reading

Manyan Labarai

Budurwa ta mutu yayin wata Gobara da ta kama cikin gidan su a Kano

Published

on

Wata Gobara da ta tashi a wani gida ta yi sanadiyyar rasuwar wata budurwa a unguwar Ja’en Sabere da ke ƙaramar hukumar Gwale a Kano da ke arewacin Najeriya, tare da ƙonewar wasu sassan gidan.

Mamallakin gidan da lamarin ya faru mai suna Saminu Abba ne ya tabbatar wa tashar Dala FM faruwar lamarin a ranar Alhamis, 16 ga watan Janairun 2025.

Ya ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe ɗaya na daren jiya Laraba, lamarin da jami’an hukumar kashe Gobara ta jihar Kano da ma ƴan Bijilanten yankin da sauran al’umma suka kai ɗauki.

“Muna cikin Bacci muka ji wata ƙara da ihun mutanen unguwa, da muka tashi muka ga Gobara ce ta tashi a wasu sassan gidan mu kuma wutar ta tare hanyar da za mu fita gashi tana ci ba ƙaƙƙautawa, “in ji Saminu”.

Ya ci gaba da cewa, “Bayan jami’an hukumar kashe Gobara da ƴan Bijilanten yankin, da sauran al’umma sun kawo musu ɗauki, ne aka fasa Gini ta gidan maƙotan su inda su shida suka fita daga gidan sai dai ƴar su budurwa mai shekaru 18 mai lalurar Sikila ta rasu”.

Mallam Saminu Abba ya ƙara da cewa, kayayyakin su na sawa da wasu tarin kayayyaki da dama ne suka ƙone ƙurmus, lamarin da ya nemi ɗaukin mahukunta da su kai musu ɗauki bisa halin da suka samu kan su a ciki.



Continue Reading

Manyan Labarai

Ba kan ta: An sace birkin jirgin sama guda 80 a Kano

Published

on

Kotun majistret mai lamba 70 da ke jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Faruk Ibrahim Umar, ta aike da wasu mutane gidan ajiya da gyaran hali bisa zargin su da haɗa baki da Sata.

Ƙunshin zargin da ake yi wa mutanen ya ayyana cewar, a ranar 11 ga watan 12 na shekarar da ta gabata ta 2025, wani mutum mai suna Otaru Bashir ma’aikaci a kamfanin sifirin jiragen sama na Azman, ya yi ƙorafi cewar mai gadin kamfanin nasu ya haɗa baki da wasu mutane sun sace musu birkin jirgin sama guda 80.

Ana dai zargin mutanen ne da sace waɗannan barakun wato birkin jirgin sama guda tamanin a filin jirgin tashi da saukar jiragen sama na Malam Aminu Kano.

Mutanen da ake zargin sun hadar da Nuhu Auwalu da Yakubu Bala da Emanuel Luka, sai kuma safiyanu Abdullahi.

Ko da aka karanta wa mutanen ƙunshin zargin da ake yi musu dukkaninsu sun musanta, a nan ne kotun ta aike da mutanen gidan gyaran hali tare da sanya ranar 11 ga watan gobe dan sauraron shaidu akan shari’ar.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewar, yayin zaman kotun an ambata cewar, binciken ƴan sanda ya bayyana cewar kimar kayan ya kama Naira miliyan dari da arba’in, sai dai yayin bincike an gano birkin jirgin guda uku a hannun wanda ake zargi na uku mai suna Yakubu Bala.



Continue Reading

Trending