Labarai
Rahoto: Lauyan Abduljabbar ya bukaci kotu ta sake shi saboda rashin hujja
Babbar kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a Kofar Kudu, karkashin mai shari’a Ibrahim Sarki Yola, ta sanya ranar 29 ga watan Agusta, domin ci gaba da shar’ar Malam Abduljabbar Nasiru Kabara.
A zaman kotun na ranar Alhamis, lauyan Abduljabbar, Barista Ibrahim Salihu Paki, ya gabatar da martini a kan kalubalentar wanda ake tuhuma, yayin da lauyoyin gwamnati, sun mika wa kotun takardun martaninsu.
Domin jin cikakken rahoton saurari wannan.
Labarai
Dilolin Wiwi sun yanki mai unguwa da Wuƙa, tare da cizon shi a hannu, kan ya shana su sha da siyar da wiwi a Kano
Wasu matasa da ake zargin ƴan Daba ne, kuma dilolin Wiwi, sun kai wa mai unguwar yankin Bachirawar Tukwane ƙarshen kwalta hari da muggan makamai.
Tun farko dai mai unguwar yankin Malam Mustapha ya shawarci matasan ne, da su dai na ɗaurin tabar Wiwi, da siyar wa a kofar gidajen mutane lamarin da ya tunzura matasan.
Matasan dai sun rutsa mai unguwar Bachirawar ne inda suka yi yunƙurin hallaka shi, bayan da suka yanke shi da Wuƙa, tare da cizon sa a Hannu, sai dai ‘yan ƙungiyar bijilante na yankin sun kawo masa ɗauki inda suka kama wani matashi mai laƙabin Kokuwa.
A lokacin ne kuma mutanen yankin suka yi yunƙurin ɗaukar doka a hannu, sai dai mai unguwar Bachirawa Malam Mustapha dan Bachirawa Gabas Malam Abdulkadir Dandiyo, sun kuɓutar da matashin inda aka mika shi ofishin ƴan sanda, ragowar matasan suka tsere.
Shugaban kungiyar ci gaban al’ummar yankin Dakta Jibrin Sagir, ya ce a shirye suke su tinkari duk wani ɓata gari a yankin da yake addabar su.
Labarai
Mata ku ƙara kula da tsaftar jikin ku a gidan auren ku – DCG Dr. Khadijah Sagir Sulaiman
Mataimakiyar babban kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano a ɓangaren Mata, DCG Dakta Khadijah Sagir Sulaiman, ta shawarci matan aure da su ƙara kulawa da tsaftar jikin su musamman kan abinda ya shafi bakunansu, da kuma gaɓoɓin da suke riƙe Gumi a wannan yanayi na zafi da ake ciki.
Dakta Khadijah Sagir, ta bayyana hakan ne yayin rangadin bibiyar auren gatan da gwamnatin jihar Kano ƙarkashin Injiniya Abba Kabir Yusuf, tayi a baya, wanda ta fara da ƙaramar hukumar Dawakin Kudu a jiya Lahadi, ina zaman ya gudana a ofishin Hisbah na ƙaramar hukumar.
DCG Khadijah, ta kuma ce matuƙar matan auren za su ƙara kulawa da tsaftar jikin nasu, hakan ka iya taimaka musu wajen ƙara wanzuwar zaman lafiya a tsakanin su da mazajen su.
Da take nata jawabin mataimakiyar kwamandan Hisbah ta ƙaramar hukumar Dawakin Kudu a ɓangaren mata Malama Saratu Sheikh Nasiru Kabara, cewa ta yi, ziyarar rangadin abu ne da tayi farin ciki, kasancewar bata taɓa samun makamanciyar ziyarar ba sama da shekaru 15 da fara aikin ta a can.
Wakiliyarmu Hadiza Balanti Ceɗiyar ƴan Gurasa ta rawaito cewa, yayin ziyarar rangadin bibiyar auren gatan Dakta Khadijah Sagir Sulaiman, ta kuma rarraba wa matan auren kayan goge baki, da kuma abubuwan da ke ɗauke sansanar jiki mara daɗi wato alumun, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa.
Labarai
Kwamitin bincike kan tsohuwar gwamnatin Ganduje ya fara zama.
Kwamitin da gwamnatin jahar kano ta kafa dan binciken gwamnatin Ganduje, ya bayyana irin sigar da masu korafi za su gabatar da ƙorafi a gaban kwamitin.
Gwamnatin jahar kano ta kafa kwamitin karkashin jagorancin mai Shari’a Faruk Lawan, dan bincike akan zargin da gwamnati mai ci take yiwa gwamnatin da ta shude akan yadda akayi tasarrafi da dukiyar jahar Kano.
A yayin zaman kwamitin mai Shari’a Faruk Lawan, ya bayyana cewa duk wani mai korafi zai rubuto korafinsa a takadda, domin gabatar wa a gaban kwamitin.
Gwamnatin dai ta kafa kwamatoci guda 2 dan bincike akan yadda akayi tassarifi da dukiyar jahar kano, da kuma abin da ya janyo ɓatan ƙananan yara, da rikice-rikicen siyasa wadanda akayi zargin sun faru a tsawon shekaru takwas na gwamnatin Ganduje.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su