Connect with us

Siyasa

Kwankwaso ba shi da kudi bai taba satar kudin gwamnati ba yafi kowa farin jini a 2023 – Buba Galadima

Published

on

Jigo a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, Buba Galadima, ya ce, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso, shi ne dan takarar shugaban kasa mafi farin jini kafin zaben 2023.

Da ya ke magana a shirin safe na Arise News, Galadima, ya ce, duk da cewa Kwankwaso ba shi da kudi domin bai taba satar kudin gwamnati ba, amma shi ne dan takarar da zai doke kowa a zaben 2023.

A cewar Galadima: “Dabararmu ita ce za mu nunawa ‘yan Najeriya cewa, dan takara mafi farin jini idan zabe ya gudana shi ne Kwankwaso.

“Kwankwaso ba shi da kudin da zai yi yakin neman zaben shugaban kasa saboda bai saci dukiyar jama’a ba.

“Kowa a fadin duniya ya san cewa Kwankwaso ne dan takarar da ya fi farin jini, Kwankwaso ya na da sihirin da zai magance matsalolin ‘yan Najeriya.”

Ya kuma caccaki shugaban kasa Muhammadu Buhari kan karramawar da aka yi wa ‘yan Najeriya. In ji Dailiy Post.

Galadima ya ce, ya kamata a ce yawancin wadanda aka karrama sun kasance a gidan yari.

Ya kara da cewa “Mutane 440 da Buhari ya ba lambar yabo ta kasa su kasance a gidan yari, a bayar da wadannan kyaututtukan ga mutanen da suka yi ritaya ba tare da wata aibu ba.”

Siyasa

Mun ƙudiri aniyar gyara tarbiyyar Matasa a jahar mu – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin Kano tasha alwashin ci gaba da magance matsalar tsaro musamman wajen kawo karshen kwacen waya da harkar Daba da ake fama dashi a jihar kano.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ne ya bayyana hakan a yayin karɓar baƙuncin mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero, a fadar fadar gwamnatin Kano, a wani ɓangare na bikin hawan Nassarawa, da ya gudana a yau Juma’a.

Abba Kabir, ya kuma ce duk da matsalolin da gwamnatin Kano ta fuskanta a baya na harkar shari’a, amma hakan bai hana ta cika alkawarin da ta ɗauka ga al’ummar jihar kano a yakin neman zaben shekarar 2023 da ta gabata ba.

Ya ƙara da cewa gwamnatinsa ba ta tsaya ba sai da ta yi kokarin magance matsalar da harkar Ilimi ke fama dashi wajen gyara makarantu da fitar da ɗalibai kasahen waje dan karo Ilimi kyauta.

“Gwamnatin mu ta bijiro da tsarin tallafawa masu harkar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da harkar Daba, da sana’oin dogaro da kai domin kawo karshen Daba a jihar kano, “in ji Gwamna Abba Kabir”.

Hawan Nasarawa dai hawa ne da ake sada zumunci a tsakanin masarautar Kano da gwamnatin Jihar Kano, da kuma al’ummar jihar, wanda da aka saba gudanar da shi a duk rana ta uku, na bikin ƙaramar Sallah, da Babba.

Da yake jawabi tunda farko mai martaba sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yabawa gwamnatin Kano akan tsarin da ta fito dashi na ciyar da al’ummar jihar kano gaba, musamman ma tsarin ciyarwar azumi da tayi ga mabukata a watan Ramadan da ya gabata.

Ya ci gaba da cewa, “Wannan ciyarwar ga al’umma tsari ne da ya kamata ya ɗore domin rage raɗaɗi da yunwa da ake fama da ita; muna shawartar Gwamnatin Kano, da ta saka ido sosai wajen kawo ƙarshen Daba da ƙwacen waya da hawa doki ana sukuwa ba bisa ka’ida ba, “in ji Sarkin”.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito mana cewa, Sarkin ya kumashawarci gwamnatin Kano, da ta ƙara dagewa wajen ci gaba da tallafawa Ilimin ɗalibai da ke fadin jihar kano, da sauran ayyuka da za su kawo wa jihar kano ci gaba.

Continue Reading

Siyasa

Gwamnan Kano ya sake naɗa Ogan ɓoye muƙami da wasu mutane takwas

Published

on

A ƙoƙarin sa na ci gaba da kawo cigaba a jihar sa Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sake naɗa Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, a matsayin mai bashi shawara a kan harkokin matasa da wasanni, tare da naɗa wasu mutane takwas waɗanda za su taimaka masa a fannoni daban-daban.

Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Litinin, ya ce Gwamnan ya amince da naɗa mutanen ne kamar haka;

An naɗa Farfesa Ibrahim Magaji Barde, a matsayin mai bai wa gwamnan shawara na musamman a kan harkokin tattara kuɗaɗen shiga (IGR).

Sai kuma Dr. Abdulhamid Danladi, da aka naɗa shi a matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman kan harkokin kasashen waje na II.

An kuma naɗa Engr. Bello Muhammad Kiru, mai bashi shawara na musamman kan albarkatun ruwa.

Yayin da aka sake naɗa Ambasada Yusuf Shuaibu Imam (Ogan Boye) a matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman a kan harkokin matasa da wasanni a jihar.

Har ila yau, Dr. Nura Jafar Shanono, shi kuma an ɗauke shi daga mai ba da shawara na musamman kan albarkatun ruwa zuwa Manajan Darakta, a ma’aikatar Ruwa da Gine-gine (WRECA) ta jihar Kano.

Shi kuwa Baba Abubakar Umar, ya samu sauyi daga mai bai wa gwamna Kano shawara na musamman ga harkokin makarantu masu zaman kansu, zuwa ma’aikatar dake kula da ma’aikatan wucin gadi.

An kuma nada Hon. Nasir Mansur Muhammad, a matsayin shugaban hukumar , ƙanana da Matsakaitan Masana’antu (SMEs).

Yayin da Aminu Hamidu Bako Kofar Na’isa ya zama mataimakin shugaban Hukumar kula da Albarkatun Noma da Raya Karkara ta Kano (KNARDA).

Shi kuwa Engr. Mukhtar Yusuf, an naɗa shi a matsayin mataimakin shugaban hukumar kula Albakatun ruwa Ruwa da Gine Gine (WRECA).

Sanusi Bature ya kuma ce, naɗin ya fara aiki ne nan take, inda Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kuma taya su murna tare da fatan alkhairi.

Continue Reading

Hangen Dala

Gaya Ajingi Albasu:- Dan majalisa ya raba kayan abinci

Published

on

Dan majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu Dakta Ghali Mustafa Fanda ya fara rabon tallafin kayan abinci ga al’ummar kananan hukumomin uku.

 

Yayin rabon tallafin kayan abincin, Dakta Ghali Mustafa yace yayi rabon tallafin ne domin fara sauke nauyin al’ummar da yake wakilta.

 

” Wannan tallafi zamu bayar da shi ne domin fara sauke nauyin al’ummar da suka zabe mu, kuma wannan shi ne karon farko, kuma yayi daidai da bukatar al’umma a yanzu, shiyasa muka fara da tallafin kayan abinci”.

 

“A cikin wannan tallafi mutane kimanin dubu ashirin ne zasu amfana, wanda zamu bayar da buhunan Shinkafa da Gero da Garin masara.”

 

Haka kuma ɗan majalisar ya bayar da tallafin Naira miliyan ashirin ga matasan kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu.

 

Sai kuma ɓangaren dalibai mata, wanda shima a yau dan majalisar ya dauki nauyin karatun dalibai mata guda 60 a bangaren lafiya.

 

Haka kuma cikin jawabin nasa Hon Ghali ya kuma ce nan gaba kadan zai bayar da tallafin taki ga manoma, da kuma farfaɗo da dukkanin rijiyon burtsatse na kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu a wani mataki na samar da ruwan sha.

 

Da yake nasa jawabin mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam Gwarzo wanda ya samu wakilcin mai baiwa Gwamna Shawara kan harkokin siyasa Hon Sunusi Surajo Kwankwaso kira yayi ga sauran wakilan al’umma da suyi koyi da Dakta Ghali Mustafa Fanda wajen ayyukan alkhairi da kuma jin kan al’umma.

 

Haka kuma Hon Sunusi Surajo ya yabawa dan majalisar bisa bayar da tallafin ga ƙananan hukumomin uku.

 

Taron dai wanda ya gudana a cikin Islamic Centre na karamar hukumar Gaya ya samu halartar manya, da kuma jagororin yankunan uku, kuma nan take Dan majalisar Tarayya Dakta Ghali Mustafa ya fara rabon tallafin

Continue Reading

Trending