Connect with us

Siyasa

Kwankwaso ba shi da kudi bai taba satar kudin gwamnati ba yafi kowa farin jini a 2023 – Buba Galadima

Published

on

Jigo a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, Buba Galadima, ya ce, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso, shi ne dan takarar shugaban kasa mafi farin jini kafin zaben 2023.

Da ya ke magana a shirin safe na Arise News, Galadima, ya ce, duk da cewa Kwankwaso ba shi da kudi domin bai taba satar kudin gwamnati ba, amma shi ne dan takarar da zai doke kowa a zaben 2023.

A cewar Galadima: “Dabararmu ita ce za mu nunawa ‘yan Najeriya cewa, dan takara mafi farin jini idan zabe ya gudana shi ne Kwankwaso.

“Kwankwaso ba shi da kudin da zai yi yakin neman zaben shugaban kasa saboda bai saci dukiyar jama’a ba.

“Kowa a fadin duniya ya san cewa Kwankwaso ne dan takarar da ya fi farin jini, Kwankwaso ya na da sihirin da zai magance matsalolin ‘yan Najeriya.”

Ya kuma caccaki shugaban kasa Muhammadu Buhari kan karramawar da aka yi wa ‘yan Najeriya. In ji Dailiy Post.

Galadima ya ce, ya kamata a ce yawancin wadanda aka karrama sun kasance a gidan yari.

Ya kara da cewa “Mutane 440 da Buhari ya ba lambar yabo ta kasa su kasance a gidan yari, a bayar da wadannan kyaututtukan ga mutanen da suka yi ritaya ba tare da wata aibu ba.”

Hangen Dala

Take hakki:- Matakin Amnesty game da kama wasu ‘yan jarida a Kano

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Amnesty International, ta yi ala-wadai da cin zarafin ‘yan jarida biyu a Kano, wato mawallafin jaridar kano Times, Buhari Abba da kuma Isma’il Auwal.

Cikin sanarwar sa Ƙungiyar ta wallafa a shafin ta na facebook,
ta ce babu shakka abin da rundunar ‘Yansandan jihar Kano ta yi bisa umarnin Kwamishinan yaɗa labaran jihar, Ibrahim Waiya abin takaici ne.

Rundunar ‘Yansandan jihar Kano dai ta gayyaci Buhari Abba zuwa sashin binciken manyan laifuka (CID) ne, harma kuma ta tsare shi na tsawon awanni.

Kuma dai ana tuhumar mutanen biyun ne da zargin ɓata sunan kwamishinan, ta hanyar wani ra’ayi da jaridar ta wallafa wanda Isma’il Auwal ya rubuta.

Kungiyar ta Amnesty ta ce duk ba zata lamunci duk wani yunƙuri na takewa waɗannan ‘Yan jarida haƙƙinsu ba.

A ƙarshe ƙungiyar taja hankalin gwamantin kano da kuma rundunar ‘Yansandan jihar, da su guji yunƙurin daƙile ‘yancin faɗin albarkacin baki.

Continue Reading

Baba Suda

Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.

 

Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.

 

Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Continue Reading

Labarai

Tsohon shugaban majalisar Dattawa Ahmad Lawan ya ƙaryata ficewar sa daga APC zuwa SDP

Published

on

Tsohon shugaban majalisar Dattawa Ahmad Lawan, ya musanta wata jita-jita da ake yaɗawa kan cewar ya fice daga cikin jam’iyyar APC mai mulki a ƙasa, zuwa SDP, al’amarin da ya ce bashi da tushe ballantana makama.

A cikin wata sanarwar da mashawarci na musamman ga tsohon Sanatan a kafafen yaɗa labarai Ezrel Tabiowo, ya fitar a jiya Lahadi, ta ce jita-jitar da ake yaɗawa na cewar Ahmad Lawan ya fice daga jam’iyyar ta APC, ƙarya ce tsagwaronta.

Jaridar Daily trust ta ruwaito cewar, sanarwar ta kuma ce, har yanzu Ahmad Lawan ɗan Jam’iyyar APC ne, kuma yana biyayya ga jam’iyyar, wadda yake alfahari da ita.

Continue Reading

Trending