Connect with us

Wasanni

Qatar 2022: Duk da rauni Belgium ta sa Lukaku a tawagar ta

Published

on

An saka Romelu Lukaku a cikin ‘yan wasa 26 da Belgium za ta wakilci kasar a gasar cin kofin duniya ta Qatar, duk da raunin da ya ji.

Babban koci Roberto Martinez ya yi gargadin cewa dole ne Lukaku ya nuna koshin lafiyarsa a matakin rukuni idan har ana so a saka shi a cikin tawagar, wanda da alama dan wasan ya yi.

Dan wasan da ya kafa tarihi a Belgium, Lukaku, wanda aro a Inter daga Chelsea, ya dawo daga jinyar raunin da ya samu, inda ya fito daga benci inda ya zura kwallo a ragar Viktoria Plzen a gasar cin kofin zakarun Turai ranar 26 ga watan Oktoba.

Duk da haka, wannan shine daya daga cikin wasanni biyu kacal da dan wasan mai shekaru 29 ya gudanar tun watan Agusta, inda wasansa na karshe ya kasance ranar 29 ga Oktoba da Sampdoria.

A ranar 23 ga watan Nuwamba ne Belgium za ta fara gasarta da Canada, kafin ta kara da Morocco da Croatia a sauran wasanninsu na rukunin F.

Tawagar Belgium: Koen Casteels (Wolfsburg), Thibaut Courtois (Real Madrid), Simon Mignolet (Club Brugge); Toby Alderweireld (Royal Antwerp), Timothy Castagne (Leicester City), Zeno Debast (Anderlecht), Leander Dendoncker (Aston Villa), Wout Faes (Leicester City), Thomas Meunier (Borussia Dortmund), Arthur Theate (Rennes), Jan Vertonghen ( Anderlecht); Yannick Carrasco (Atletico Madrid), Kevin De Bruyne (Manchester City), Thorgan Hazard (Borussia Dortmund), Amadou Onana (Everton), Youri Tielemans (Leicester City), Hans Vanaken (Club Brugge), Axel Witsel (Borussia Dortmund); Michy Batshuayi (Fenerbahce), Charles De Ketelaere (Milan), Jeremy Doku (Rennes), Eden Hazard (Real Madrid), Romelu Lukaku (Inter), Dries Mertens (Galatasaray), Lois Openda (Lens), Leandro Trossard (Brighton and Hove). Albion)

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending