Connect with us

Ƙasashen Ƙetare

Mutumin da ya yi karyar ya mutu an sake kama shi

Published

on

Kotu ta yanke hukuncin cewa wani mutum da aka kama a wani asibiti a Scotland a bara, dan kasar Amurka ne mai suna Nicholas Rossi, bayan an kammala bincike. Mutumin ya yi iƙirarin cewa shi ne wanda aka yi masa kuskure, kuma ya dage cewa sunansa, Arthur Knight mai makon Nicholas Rossi. Amma Kotun Edinburgh Sheriff shaidar yatsansa sun yi daidai da na Rossi.

Hukumomi a Amurka na neman a tasa keyar Rossi, bisa zargin fyade da cin zarafi. Ana zargin cewa ya yi karyar mutuwar na sa ne kuma daga baya ya gudu zuwa kasar Scotland, domin gujewa fuskantar tuhuma. Ya shafe shekara guda a matsayin sunan shi Arthur Knight, kuma shi maraya ne daga Ireland wanda bai taba zuwa Amurka ba.

A dai watan Maris mai zuwa ne kotun za ta yanke hukuncin cewa za ta mika mutumin zuwa Amurka ya fuskanci hukunci ko akasin haka. A shekarar da ta gabata ne dai ‘yan sandan Scotland suka kama Rossi a wani asibiti bayan da aka gano zanen da yake a jikin hannun sa na Tatto ya yi kama da nasa a lokacin da ake bashi kulawa a asibitin bayan ya sha fama da cutar Covid 19.
Sai dai a gwajin shaidar zanen ya tsayar sa ta yi daidai da wanda ake tuhuma, kamar yadda kwararriyar mai bincike Lisa Davidson ta shaidawa kotu.

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji Sun yi juyin Mulki a Gabon

Published

on

Sojoji sun bayyana a gidan talabijin na kasar Gabon tare da sanar da karbi mulki.

Sun ce sun soke sakamakon zaben da ka gudanar ranar Asabar, inda aka ayyana shugaba Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukumar zaben ta ce Mr Bongo ya samu nasara ne da kasa da kashi biyu bisa uku na kuri’un da aka kada a zaben da ‘yan adawa suka ce an tafka magudi.

Sun Kuma ce Hambarar da shi zai kawo karshen mulkin shekaru 53 da iyalan gidansu ke yi a Gabon.

Sojoji 12 ne suka bayyana a gidan talabijin dake sanar da soke sakamakon zaben tare da rusa dukkan hukumomin kasar.

Daya daga cikin sojojin ya fada a tashar talabijin ta Gabon 24 cewa, “Mun yanke shawarar kare zaman lafiya ta hanyar kawo karshen mulkin da ake yi a yanzu.”

Mr Bongo ya hau karagar mulki lokacin da mahaifinsa Omar ya rasu a shekara ta 2009.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji sunyi juyin Mulki a jamhuriyar Nijar

Published

on

Rahotanni daga jamhuriyar Nijar na cewa Sojojin Kasar sun yi juyin Mulki, tare da sanar da kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum.

Cikin sanarwar da suka bayar a gidan telebijin din Kasar, jagoran tawagar sojojin Kanal Amadu Abdramane yace “mun kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum tare da karbe dukkanin Wani Iko”.

Sojojin dai sun bayar da dalilin halin rashin tabbas da Kuma Matsin tattalin arziki a kasar.

Tuni dai sojojin suka garkame dukkanin iyakokin Kasar tare da Sanya dokar takaita zirga zirga daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Tun a safiyar laraba ne dai aka wayi gari da fara wancan yunkuri, Wanda yanzu haka ta tabbata, Kasar Nijar na hannun sojoji, Wanda shi ne Karo na hudu ana gudanar da juyin mulkin a jamhuriyar Nijar.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

An tsaurara tsaro a fadar shugaban Kasar Nijar

Published

on

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar, na nuni da cewa dakarun da ke gadin fadar shugaban ƙasa sun rufe duk wata hanyar shiga fadar a wani lamari da ba a kai ga ganowa ba.

Sai dai rahotanni na cewa yanzu haka wasu daga cikin tsofaffin shugabannin ƙasar ta Nijar na tattaunawa da sojojin domin sasanta lamarin.

Karin bayani nan tafe….

Continue Reading

Trending