Siyasa
Rikicin cikin PDP: Zan tallafawa da Obi kayan aiki a zaben 2023 – Wike

Gwamna Nyesom Wike na jihar Rivers a ranar Alhamis ya yi alkawarin tallafawa Peter Obi, , dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour Party, LP.
Wike ya ce zai bada tallafin kayan aiki a lokacin yakin neman zaben Obi a jihar Ribas.
Ya yi alkawarin baiwa Obi goyon baya a lokacin da ya furta hakan a wurin bikin kaddamar da gadar sama ta Nkpolu-Oroworokwo a Fatakwal.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa, Obi ya na da abin da ake bukata domin zama shugaban Najeriya.
A cewar Wike: “Duk lokacin da kuke son yin yakin neman zabe a jihar, ku sanar da ni, duk tallafin dabaru, za mu ba ku.”
Obi, da abokin takararsa, Datti Baba-Ahmed, da wasu mambobin kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na LP, sun je Rivers domin kaddamar da gadar sama ta 9 da gwamnatin Wike ta yi.
A cikin ‘yan watannin da suka gabata, Wike ya na mu’amala da jiga-jigan wasu jam’iyyun siyasa.
Wannan mataki na Wike dai na iya kasancewa ga korafe-korafen sa da shugabancin jam’iyyar PDP, biyo bayan kayen da ya sha a zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar.

Siyasa
Rurum ya sanar da ficewa daga jam’iyyar NNPP zuwa APC a zauren Majalisar Wakilai

Shugaban majalisar Wakilai ta Ƙasa Tajudden Abbas, ya karanta takardar ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Rano, Kibiya da Bunkure, RT. Honarable Kabiru Alhassan Rurum, ta ficewarsa daga Jam’iyyar NNPP zuwa Jam’iyyar APC, a hukumance.
Tajuddeen Abbas, ya karanta takardar sauyin sheƙar da Rurum din yayi a harabar Majalisar, a zamanta na yau Alhamis.
Wannan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da mai bai wa Rurum, shawara na musamman akan shafukan sada zumunta Fatihu Yusuf Bichi, ya fitar a ranar Alhamis 15-05-2025.
Tun dai a baya an jiyo yadda Honarable Kabiru Alhassan Rurum, ya sanar da ficewar sa daga jam’iyyar NNPP zuwa APC, wanda a yanzu na tabbatar da ficewar tasa a hukumance a zauren Majalisar Wakilai ta ƙasa.

Hangen Dala
Yau shugaban kasa zai dawo daga Faransa

Bayan ziyarar aiki ta kusan mako biyu Zuwa kasar Faransa a yau litinin ake saka ran shugaban kasa zai dawo gida Nigeria.
Cikin sanarwar da hadimin shugaban kasar kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fitar ya ce kowa ne lokaci daga yanzu shugaban kasa Asuwaju Bola Tinubu zai sauka a Nigeria domin cigaban da harkokin mulkin kasar.

Hangen Dala
Kofar APC a bude take ga masu shiga – Abdullahi Abbas

Jamiyyar APC a Jihar Kano tace Kofar ta a bude take ga dukkanin masu son shigowa jamiyyar.
Shugaban jamiyyar na Kano Hon Abdullahi Abbas ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai.
Abbas yace labarin dake yawo cewa akwai wadanda ke Shirin shigowa jamiyyar, su sani Kofar APCn a bude take tare da maraba ga dukkanin wadanda zasu shigo.
Koda dai Abdullahi Abbas yace shigowa APC ba zai hana tuhuma kan zargin cin hanci da rashawa ba, koma kaucewa hukumar EFCC da ICPC.
A baya bayan nan ne dai aka rinka yada cewa mabiya jamiyyar NNPP kwankwasiyya na Shirin shiga jamiyyar APC tare da madugun ta Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su