Connect with us

Manyan Labarai

Da Muninsa: Manchester United ta yanke hulda da Ronaldo

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta sallami dan wasan Portugal, Cristiano Ronaldo, nan take.

Matakin dai ya biyo bayan wata tattaunawa mai cike da cece-kuce da dan wasan mai shekaru 37 ya soki kungiyar kuma ya ce, ba ya mutunta kocin kungiyar Erik ten Hag.

Bangarorin biyu sun bayyana cewa sallamar ta Ronaldo “an amince da juna nan take”.

Sanarwar da Manchester United ta fitar ta ce “Kungiyar ta gode masa saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar tsawon shekaru biyu a Old Trafford.”

Sun yi fatan alheri ga “shi da iyalinsa a nan gaba” kuma sun kara da cewa “kowa a Manchester United ya ci gaba da mai da hankali kan ci gaba da kai kungiyar a karkashin Erik ten Hag da kuma yin aiki tare, domin samar da nasara a filin wasa”.

Ronaldo ya na tare da Portugal a gasar cin kofin duniya da ake yi a Qatar kuma ya na shirin jagorantar su a wasan farko na rukunin H da Ghana ranar Alhamis.

“Bayan tattaunawa da Manchester United mun amince tare da kawo karshen kwantiragin mu da wuri,” in ji wata sanarwa daga dan wasan.

“Ina son Manchester United kuma ina son magoya baya, hakan ba zai taba canzawa ba. Duk da haka, ya  na jin lokacin da ya dace da ni domin neman sabon kalubale.

“Ina yiwa kungiyar fatan samun nasara a sauran kakar wasanni da kuma nan gaba.”

Hangen Dala

Zargin Almundahana:- An kama jami’in gwamnatin Kano

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da kama Tasiu Al’amin-Roba, babban mataimaki na musamman (SSA), ga gwamnan jihar kano da kuma wani Abdulkadir Muhammad bisa zargin su da karkatar da kayan abincin tallafi a jihar Kano.

 

Kwamishinan ‘yan sandan, Hussaini Gumel, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN hakan a wata hira ta wayar tarho a ranar Lahadi cewa, an kama wadanda ake zargin ne a wani dakin ajiyar kaya da ke Sharada dauke da jakunkuna sama da 200.

 

Ya kara da cewa wadanda ake zargin sun yi awon gaba da shinkafa da masara a ma’ajiyar da ke Sharada.

 

“Tun daga lokacin ne muka fara bincike mai zurfi don gano buhunan masara ko shinkafa nawa aka diba aka sayar da su,” inji shi.

 

Gumel ya ce za a gurfanar da mutanen biyu a gaban kotu bayan kammala bincike .

Continue Reading

Hangen Dala

An yiwa kasafin Kudin 2024 karatu na biyu

Published

on

Majalisar Dattawan Najeriya da ta Wakilai sun yi wa kasafin kuɗin ƙasar na 2024 karatu na biyu ranar Juma’a kwana biyu bayan Shugaba Bola Tinubu ya gabatar musu da shi.

A ranar Laraba ne Tinubu ya je majalisar tare da gabatar da naira tiriliyan 27.5 a matsayin kasafin abin da gwamnatinsa za ta kashe a 2024, kuma ya nemi ‘yan majalisar su gaggauta amincewa da shi.

Sai dai shugaban bai bayyana adadin abin da kowace ma’aikata da hukumomin gwamnati za su samu ba a lokacin da ya yi gabatarwar, abin da ya jawo cecekuce da muhawara a ƙasar.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito ‘yan majalisar na kokawa yayin muhawarar da suka yi ranar Juma’a game da ƙarancin bayanai kan kasafin, wanda suka ce ya sa sun mayar da hankali ne kawai kan abubuwan da Tinubu ya faɗa a jawabinsa.

Jam’iyyun adawa sun soki kasafin da cewa “na yaudara ne”, yayin da Shugaba Tinubu ya yi masa laƙabi da “kasafin sabunta fata”.

Continue Reading

Manyan Labarai

Hajiya Aisha Bura ta lashe zaben shugaban mata yan jarida na kasa NAWOJ

Published

on

Zaɓaɓɓiyar shugabar kungiyar mata ƴan jarida ta ƙasa Hajiya Aisha Ibrahim Bura ta alkawarta yin tafiya da kowanne bangare domin samar da hadin kai da ci gaban mambobin kungiyar.

Hajiya Aisha Bura ta bayyana hakan jim kadan bayan kammala rantsar da ita a matsayin wadda ta samu nasarar lashe zaben da aka gudanar a daren jiya.

Ta ce, akwai bukatar mambobin kungiyar su bata hadin kai don ganin ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta.

Hajiya Aisha Ibrahim Bura ta samu nasara da kuri’u 498 yayin da abokiyar takarar ta kuma shugabar kungiyar mai barin gado Hajiya Ladi Bala ta samu kuri’u 381.


Continue Reading

Trending