Connect with us

Wasanni

Neymar da Danilo ba za su buga wasanni biyu a Qatar – Brazil

Published

on

Neymar ba zai buga wasanni biyu na gasar cin kofin duniya da Brazil za ta buga ba, bayan da ya samu rauni a kafarsa ta dama, in ji likitan tawagarsu.

An maye gurbin dan wasan mai shekaru 30 a minti na 80 na wasan da suka doke Serbia da ci 2-0 a ranar Alhamis, bayan da Nikola Milenkovic ya yi masa ya yi masa keta.

Shi ma Danilo ba zai buga wasanni biyu masu zuwa ba saboda rauni a idon sawunsa.

Brazil za ta kara da Switzerland a wasansu na biyu a rukunin G ranar Litinin (16:00 GMT), kafin kuma ta kara da Kamaru ranar Juma’a mai zuwa (19:00 BST).

“Neymar da Danilo sun yi gwajin MRI a ranar Juma’a da yamma kuma mun sami rauni a idon sawun su biyu,” in ji likitan tawagar Brazil Rodrigo Lasmar.

Da yake magana bayan nasarar da suka yi da Serbia, babban kocin Brazil Tite, ya ce, suna da yakinin cewa Neymar zai ci gaba da taka leda a gasar cin kofin duniya.

Dan wasan na Paris St-Germain ya samu raunuka da dama da kafarsa ta dama a shekarun baya.

Bai buga gasar Copa America ta 2019 ba, bayan ya sha fama da rauni a idon sawunsa na dama kuma ya yi jinyar makonni da yawa a cikin 2021 da irin wannan rauni.

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending