Connect with us

Wasanni

Rauni: Ku yi watsi da jita-jitar da a ke yi a kan Benzema – Kocin Faransa

Published

on

Kocin Faransa, Didier Deschamps, ya yi watsi da rade-radin cewa dan wasan gaban Karim Benzema zai iya komawa tawagar Les Bleus ta gasar cin kofin duniya.

A cewar Deschamps, bai san yadda ake ta cece-kuce akan Benzema ba. Benzema ya na fama da rauni a gasar cin kofin duniya ta FIFA 2022.

An tilastawa dan wasan na Real Madrid ficewa daga gasar cin kofin duniya gaba daya, saboda rauni kuma Deschamps bai kira wanda zai maye gurbinsa ba duk da cewa ya iya.

Rahotanni sun bayyana cewa har yanzu Benzema yana cikin jerin ‘yan wasan da suka yi wa rajista a gasar cin kofin duniya kuma zai iya dawowa kafin a kammala gasar a Qatar.

Sai dai a yanzu Deschamps ya yi watsi da shawarar inda ya nanata cewa ya ji dadin ‘yan wasan da ke hannun sa.

Da aka tambaye shi ta hanyar zagayawa game da rade-radin da ke tattare da Benzema, Deschamps ya ce a wani taron manema labarai gabanin wasan Faransa da Tunisia a gasar cin kofin duniya a ranar Laraba: “Kai. To, ban tabbata ba [abin da zan faɗa], hakika wannan ba wani abu bane da nake tunani akai.

“Da alama kun san abubuwa da yawa game da lamarin amma da gaske ban bi wanda ke faɗin me ba.

“Na yi magana da Karim bayan ya tafi kun san halin da ake ciki, kuma mun ji tsawon lokacin da zai dauka kafin ya warke.

“Don haka ban san ainihin abin da kuke ƙoƙarin nunawa ba. Ina da ‘yan wasa 24 a cikin tawagara kuma ina farin ciki da ‘yan wasan da nake da su.

“Wasu ‘yan wasan sun bace, Kimpembe da Pogba ma sun bace, kuma ba shakka, ina magana da su.

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending