Wasanni
Ghana da Uruguay sun yi adabo da gasar cin kofin duniya

Uruguay ta doke Ghana amma dukan su sun fice daga gasar cin kofin duniya, inda suka zo na uku da na hudu bayan Koriya ta Kudu a rukunin H ta zo na biyu, duk da bajintar da Luiz Suarez ya yi.
Giorgio de Arrascaeta ne ya zura kwallayen biyun, na farko da ya zura da kai, a daya wasan na rukuni na H, Koriya ta Kudu ta doke Portugal da ci 2-1 a rukunin da ya kai ta matsayi na biyu.
Suarez, wanda kwallonsa ta hannu a haduwarsu da suka gabata shekaru 12 da suka gabata ta taka muhimmiyar rawa wajen fitar da Ghana.

Wasanni
Dembele ya tallafawa Barcelona ta kai wasan kusa da na karshe

Dan wasan gaban kungiyar kwallon kafa ta Barcelona Ousmane Dembele ne, ya zurawa Barcelona kwallo daya tilo a wasan kusa da na karshe da suka buga da kungiyar kwallon kafa ta Real Sociedad, a gasar Copa Del Rey da ke gudana a kasar ta Spain, wanda hakan ne yabawa Barcelona damar zuwa wasan kusa da na karshe a gasar.
Kawo yanzu, dan wasa Ousmane Dembele ya zurawa kungiyar kwallon kafa ta Barcelona kwallaye bakwai a kakar wasannin nan da muke ciki.

Wasanni
Kungiyar kwallon kafa ta Tottenham ta dauki aron Danjuma daga Villarreal

Kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Hotspur ta sanar da daukan aron dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Villarreal dan asalin kasar Netherlands wato Arnaut Danjuma mai shekaru 25 har zuwa karshen kakar nan da muke ciki.
Tun bayan da aka bude kasauwar saye da sayarwa na ‘yan wasanni a watan janairun nan da muke ciki, Arnaut Danjuma, shine dan wasa na farko da Tottenham Hotspur din ta dauka.
Tottenham Hotspur ta na mataki na biyar a teburin gasar firimiyar kasar Ingila ta shekarar 2022 zuwa 2023 da muke ciki.

Wasanni
Kungiyar kwallon kafa ta Everton ta kori Lampard

Tsohon da wasan kasar Ingila mai shekaru 44 Lampard ya karbi aikin horas da kungiyar kwallon kafa ta Everton a watan janairun shekarar 2022 da ta gaba ta, bayan sallamar mai horas da ita na wancan lokacin Rafael Benitez.
Everton dai ta yi rashin nasara a wasanni tara cikin wasanni 12 da ta buga a gasar Firimiyar kasar Ingila ta shekarar 2022 zuwa 2023 da muke ciki.
A ranar Asabar din da ta gabata dai kungiyar kwallon kafa ta Everton ta yi rashin nasara a karawar da ta yi da kungiyar kwallon kafa ta West Ham United, wanda hakan yasa ta ke mataki na 19 da maki 15 a teburin gasar ta bana.

-
Nishadi3 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi3 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai2 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Lafiya8 months ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi3 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano