Connect with us

Addini

Abubuwan da ya kamata mu yi a lokacin da muke cikin fushi.

Published

on

Litattafan Addinin Musulunci
  • Fushi daga shaidan yake
  • Mu yawaita zama da Alwala da kuma ambaton Allah
  • Mu guji daukar hukunci lokacin da muke cikin fushi .

A shafin sa na facebook, Falalu Dorayi yayi tsokaci kan abubuwan dake jawo fushi, da kuma hanyoyi kauce musu kamar haka

Tasirin fushi a zucivar Dan Adam na iva haifar da masifu da abubuwa marasa dadi iri iri, ciki harda kisan kai.

Duk Lokacin da Dan Adam yake cikin fushi ko wani vanayi na bacin rai,Tabbas wannan mutumin na samun bakuncin Shaidan kusa da zuciyarsa, kuma duk hukuncin da zai yi a wannan lokacin ba zai zamo mai inganci ba,ma’ana zai dauki hukunci mara dadi.

Idan muka samu kanmu a irin wannan yanayin Ma’aiki Rasulullah (SAW) Ya bamu mafita:

  1. Mu daura Alwala
  2. Mu yawaita fadin “A’udhu billahi minashaytaan-ir-rajeem”
  3. Idan a tsaye muke mu zauna, idan bamu daina fushin ba kuma mu kwanta.

Kada mu biyewa zuciya, mu kasance masu  hakuri.

Rahoto: Koyi da halayen Annabi ne nuna tsantsar kaunar sa – Limamin Tukuntawa

Ubangiji  Yana son masu hadiye fushi da yafiya lokacin da aka fusata su.

Mu duba; (Ali Imran 3:134)

Allah Yasa mu dace

Addini

Rahoto: Gaɓoɓi shaida ne ga abinda mutum ya aikata ranar Alkiyama – Limamin Tukuntawa

Published

on

Babban limamin masallacin Juma’a na Masjidul Quba dake unguwar Tukuntawa, Malam Ibrahim Abubakar Tofa, ya ce, akwai bukatar musulmi su yi kokarin aikata alkhairin, domin Gaɓoɓinsu, zasu bayar da shaidar duk abinda suka yi a ranar Alkiyama.

Malam Ibrahim Tofa, ya bayyana hakan ne, a zantawarsa da wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki.

Akwai cikakkiyar a hudubar a muryar da ke kasa.

Continue Reading

Addini

Rahoto: Mu dauki aikin alheri wanda ba za mu daina yi ba – Limamin Tukuntawa

Published

on

Limamin masallacin Juma’a na Masjidul Quba dake unguwar Tukuntawa, Mallam Ibrahim Abubakar Tofa, ya ce, akwai bukatar mutum ya dauko aikin alheri wanda zai ci gaba yi ba tare da ya daina ba.

Mallam Ibrahim Tofa, ya bayyana hakan ne, a zantawarsa da wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki.

Domin jin cikakken rahoton saurari wannan.

Continue Reading

Addini

Rahoto: Al’umma su haɗa kan su domin samar da ci gaba – Limamin sabuwar Gandu

Published

on

Limamin masallacin Juma’a na Sheikh Mahmud Adam, dake sabuwar Gandu, Mallam Iliyasu Muhammad, ya ce, al’umma su haɗan su domin samar da ci gaba a tsakanin su.

Malam Iliyasu, ya bayyana hakan ne, a zantwarsa da walikin mu na ƴan Zazu, Abba Isah Muhammad.

Domin jin cikakkiyar huɗubar saurari wannan.

Continue Reading

Trending