Connect with us

Manyan Labarai

Za’a fara hako mai a jihar Nassarawa

Published

on

Kamfanin hakowa da sarrafa albarkatun man fetur na Najeriya NNPCL, yauwa bayyana cewa cikin watan Maris din 2023 ne za a fara aikin hako danyen man fetur a jihar Nassarawa.

Shugaban Kamfanin Mele Kyari ne ya bayyana hakan a shafin sa na Tuwita, inda ya ce “hakan ci gaba ne da aikin hakon mai da nufin samar da rijiyar mai ta farko a jihar”.

Ya shaida hakan a lokacin da yake karbar bakuncin tawagar fitattun yan asalin jihar ta Nassarawa, karkashin jagorancin Gwamnan jihar, Injiniya Abdullahi Sule a ofishin kamfanin da ke birnin tarayya Abuja.

Gano arzikin man a Nassarawa ya zo ne kusan wata biyar bayan da NNPC ya soma aikin hako mai a yankin Kolmani, da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe.

Tun a shekarar 2019 ne kamfanin na NNPC ya bayyana gano albarkatun man fetur a yankin na Kolmani.

Kyari ya ce “binciken da aka gudanar ya nuna cewa akwai tabbacin kasancewar albarkatun ruwa mai yawa a jihar.”

Cikin wata sanarwa ta baya-bayan nan da NNPC ya fitar, Mele Kyari ya bayyana bukatar a hanzarta gudanar da aikin, ganin cewa karkatar da kasashen duniya suka yi zuwa ga makamashi ya janyo raguwar zuba jari a bangaren mai.

Ya kamata a gaggauta yin aikin saboda kasashen duniya na janyewa daga dogaro da man fetur, idan ba haka ba, shekaru 10 daga yanzu, babu wanda zai amince ya zuba kudi a kasuwancin man fetur.” kamar yadda sanarwar ta ambato shugaban NNPC na fadi.

A cewarsa, samun hadin kai daga al’umma da yanayi mai kyau na da matukar muhimmanci wajen samun nasarar aikin, domin kaucewa irin barnar da yan bindiga ke yi wa bututan mai a yankin Neja Delta.

A martaninsa, Gwamna Sule ya taya mahukuntan kamfanin NNPC da gwamnatin tarayya murna, saboda kokarin da suka yi na ganin an soma aikin samar da mai a Kolmani da Shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar a Nuwambar 2022.

Manyan Labarai

Tsadar Rayuwa: Zanga-zanga ba ita ce mafita ba a Najeriya – Sarkin Zazzau

Published

on

Mai martaba Sarkin Zazzau Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli, ya ce tsadar rayuwar da aka samu kai yanzu a ciki zanga-zanga ba ita ce mafita ba, inda ya ce a guji yin irin abubuwan da ka iya haddasa kifar da gwamnatoci irin yadda ta faru a wasu kasashen Duniya.

Sarkin na Zazzau Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli ya bayyana hakan ne jim kadan da fitowar su daga ganawar da suka yi da shugaban kasa Tinubu, da ministoci da gwamnoni da kuma sarakunan gargajiya, a yammacin yau Alhamis.

Rahotanni dai sun bayyana cewa ganawar ta mayar da hankali ne akan hanyoyin daƙile zanga-zanga da kuma sauran matsalolin da ke addabar al’umma a ƙasa, da kuma samar da tsaro a kasa.

Dubban al’ummar ƙasa ne dai suka ƙudiri aniyar gudanar da zanga-zanga akan tsadar rayuwar da aka samu kai a ciki, wanda suka bayyana ranar 1 zuwa 10 ga watan Agusta mai kamawa, domin gudanar da zanga-zangar, don nusartar da gwamnati halin da ake ciki na ƙuncin rayuwa, kamar yadda kafar Dala FM Kano ta rawaito.

Har ila yau, Sarkin na Zazzau a wata tattaunawar sa da kafar yada labarai ta DW, ya ce duk abinda kwanciyar hankali bai kawo ba, babu makawa tashin hankali ba zai kawo ba, a don haka akwai bukatar al’umma suyi hakuri tare da bin hanyoyin da suka dace mai-makon yin zanga-zangar.

Alhaji Nuhu Bamalli, ya ƙara da cewa, ya kamata gwamnati ta tabbatar da tsaro ta yadda za’a samu zaman lafiya a kasa, wanda al’umma za su koma gona domin ci gaba da aikin noman su mai-makon a rinka basu tallafin da ba zai iya magance musu talaucin da suke ciki ba.

Continue Reading

Manyan Labarai

Mafi ƙarancin albashi N70,000 ya shafi Direbobi, Masu Gadi, da masu aikin Gida – Cewar Akpabio shugaban Majalisar Dattawa

Published

on

Majalisar Dattawa ta ƙasa, ta ce duk ma’aikatan gwamnati, da ma waɗanda ba na gwamnatin ba, irin su masu gadi, da Direbobi, da kuma masu Shara da wanke-wanke, duk sun shiga cikin sahun karɓar mafi ƙarancin albashin Naira 70,000, a Najeriya.

Shugaban majalisar dattawan Sanata Gidswill Akpabio, ne ya bayyana haka ne a zaman majalisar da aka yi na ranar Talata, bayan da majalisar ta amince da sabon ƙudirin biyan mafi ƙarancin albashi ga ma’aikata a Najeriya.

Akpabio, ya kuma ce idan mutum Tela ne kuma ya ɗauki ma’aikata, to ya sani ba zai biya shi ƙasa da Naira 70,000 ba, kuma idan uwa ce mai jariri kuma tana son ɗaukar ƴar aikin gida don kula da yaron, itama zata biya ta dai-dai da mafi ƙarancin albashin da aka amince da shi, kuma dokar ta shafi kowa da kowa.

A cewar sa, “Idan ka ɗauki direba ko mai gadi ba za ka biya su kasa da N70,000 ba, a don haka, na yi matuƙar farin ciki da aka ƙaddamar da haka, kuma a yanzu muna sa ran masu ɗaukan ma’aikata su inganta kan abin da aka kafa kowa ya bi, “in ji Akpabio”.

Har ila yau, shugaban majalisar dattawan, ya kuma taya ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa, da ma ɗaukacin ƴan Nijeriya, da majalisar Dokoki ta ƙasa, murnar wannan doka da aka kafa, wanda har ma aka rage wa’adin tattaunawar daga shekaru biyar zuwa shekaru uku.

Ya ce duba da yadda tsadar rayuwa ke ci gaba wannan kuma wani muhimmiyar doka ce, a don haka yake taya kowa murna akan ta.

A makon da akayi bankwana da shi ne dai Dala FM Kano, ta kawo muku labarin yadda shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu, ya amince da mafi ƙarancin albashi na Naira dubu 70,000, ga ma’aikata a Najeriya, al’amarin da suma ƙungiyoyin ƙwadago suka yi maraba da batun.

Continue Reading

Manyan Labarai

Na yi takaici kan rashin kulawa da makarantar Governors College – Gwamnan Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya koka tare da nuna takaicinsa bisa yadda ya sami makarantar Governors College, cikin rashin kulawa, da yadda ɗaliban makarantar suke karatu babu abubuwan zama, da yadda wasu ajujuwan suke cike da ruwa.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi wannan jawabin da yammacin yau, yayin wata ziyarar bazata da ya kai makarantar, domin ganin yadda aikin ta yake gudana, da kuma tabbatar da anyi mata aiki yadda gwamnati ta tsara.

Gwamna Abba Kabir, ya kuma ƙara da cewa, ya yi tsammanin yadda makarantar take ta waje fesfes a waje, hakan ma zai ga cikin ta amma sai ya tarar da saɓanin hakan.

“Muna kira ga manyan ƴan kasuwa da suke faɗin jihar Kano da su shigo domin tallafa wa harkar ilimi musamman makarantun firamare da na sakandire, domin ciyar dasu gaba, “in ji Abba Kabir”.

Idan ba’a manta ba, Tun a baya Dala FM Kano, ta kawo muku labarin yadda gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sanya dokar ta ɓaci akan Ilmi a jihar.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Umar Abdullahi Sheka ya rawaito cewa, gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, ya tabbatar da magance duk wata matsala da ta shafi fannin ilimi a faɗin jihar Kano.

Continue Reading

Trending