Manyan Labarai
Kano ta tsakiya= Abinda yasa har yanzu INEC ba ta sauya sunan Shekarau da Rufa’i Hanga ba – NNPP

Jam`iyyar NNPP, ta nuna damuwa game da kin amincewar da hukumar zabe ta yi da wasu sunayen da ta gabatar mata domin maye gurbin wasu daga cikin `yan takararta da suka janye.
Jam`iyyar ta ce ta kai maganar gaban alkali, kuma sau biyu kotu tana ba ta gaskiya, amma hukumar zaben ta ci gaba da yin turjiya.
NNPP, ta ce ta bi dukkan ka’idojin da doka da INEC ta shimfida wajen mika sunayen ‘yan takararta na mukamai daban-daban ciki har da kujerar sanatan Kano ta tsakiya, wadda tsohon gwamnan jihar sanata Ibrahim Shekarau, ya janye bayan ficewarsa daga jam’iyyar.
To amma, jam’iyyar ta fara zargin hukumar zabe nayi mata wasa da hankali har ma ta fara zargin ko akwai wata rufa-rufa da hukumar zaben keyi mata.
Injiniya Buba Galadima, jigo ne a jam’iyyar ta NNPP, ya shaida wa BBC cewa, su babban abin da ya dame su shi ne ko akwai wata jikakkiya tsakaninsu da hukumar zabe wadda ba su sani ba.
Ya ce, “ Duk dan Najeriya ya sani cewa Malam Ibrahim Shekarau, ya bar jam’iyyar NNPP, mun rubuta wa INEC cewa tun da Shekarau ya bar mu a bamu ranar da zamu sake zaben fitar da wani dan takarar da zai maye gurbin Shekarau.”
To amma sai INEC, ta rubuto cewa bata yarda ba, mu kuma muka fitar da dan takara muka aika musu amma suka ce ba su yarda ba,” inji shi.
Buba Galadima, ya ce daga nan suka garzaya zuwa kotu, kotu kuwa ta ce suna da gaskiya.
Ya ce, “Daga nan ne sai INEC, ta ce bata yarda ba ta daukaka kara, kotu ta gaba kuwa ta ce dole a kyale jam’iyyar da ya bari ta fitar da wani dan takara, sai suka ce sai sun sake daukaka kara zuwa kotun koli.”
Buba Galadima, ya ce ‘’ Wai shin mene ne ma bukatar INEC?”.
Bayan kujerar dan takarar sanata ta Kano ta tsakiya, akwai wasu kujerun kamar ta dan takarar sanata a jam’iyyar a Taraba ta Kudu Murtala Garba, wadanda a har yanzu hukumar zabe bata karbesu ba.
To sai dai kuma hukumar zaben ta ce bata da wata manufa game da jinkirin da ta ke yi wajen karbar sunayen masu takarar, face bukatar abi doka.
Wani babban lauyan a hukumar zaben, Tanimu Muhammad, ya shaida wa BBC cewa, ita hukumar zabe babu abin da take bukata illa kawai abi doka.
Ya ce,’’ Jam’iyyar NNPP ce ta fara gurfanar da mu gaban kotu, kuma ita kara a kan batun zabe karace da zata iya zuwa har kotun koli, shi ya sa muka tafi can don muna son sanin abin da ya kawo rikici tsakaninmu da ‘ya’yan jam’iyyar.”
Babban lauyan ya ce abin da suke nema su yi ya sabawa jadawalin da muka bayar.
Baya ga jam’iyyar NNPP, akwai wasu jam’iyyun da dama wadanda ke da irin wadannan korafi ko bukatar sauya sunayen da suke so su maye gurbin wasu ‘yan takara da suka janye, da suma suka zuba ido don ganin yadda zata kaya tsakanin hukumar zaben ta kasa da kuma jam’iyyar NNPP.

Manyan Labarai
Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.
Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a
“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.
Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.
Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Manyan Labarai
An ga watan ƙaramar Sallah a Najeriya – Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na uku ya tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya, inda za a yi karamar Sallah gobe Lahadi.
Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a yayin jawabin da ya gabatar a cikin daren Asabar ɗin nan, ya ce sun samu rahotannin ganin watan ne daga sassa daban-daban na ƙasar nan.
Alhaji Sa’ad Abubakar ya ce daga cikin guraren da aiko musu da ganin jinjirin watan na Shawwal akwai Zazzau, da kuma daga Sarkin Dutse, da Arugungu, da kuma Shehun Borno, da dai sauran gurare daban-daban na Najeriya.
Ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su gabatar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali, tare da taimaka wa mabuƙata.
Tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewa, biyo bayan sanarwar fadar mai alfarma Sarkin Musulmi, ya kasance ranar Lahadi take 1 ga watan Shawwal na shekarar 1446, wato ranar ƙaramar Sallah.

Manyan Labarai
Shugaba Tinubu da Sifeton Ƴan Sanda ku bi wa mutanen mu da aka yi wa kisan gilla hakƙin su – Rt. Hon. Rurum

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Rabo, Kibiya da Bunkure, Kabiru Alhassan Rurum, ya bayyana kaɗuwar sa bisa kisan gillan da aka yi wa wasu Mafarauta su kusan 16, a garin Uromi da ke jihar Edo, a lokacin da suke hanyar su ta komawa Kano daga jihar Rivers.
Honarable Kabiru Rurum, ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da aka aikowa Dala FM Kano a ranar Asabar, ya ce daga cikin mutanen da aka ƙona akwai mutum 11 da suka fito daga mazaɓun yankin sa na Kibiya da Bunkure, inda wasu 6 suka samu muggan raunuka suna karɓar Magani yanzu haka a jihar Edo.
A cewar Ɗan Majalisar, “Wannan abu da matasan garin Uromi a jihar Edo, suka yi ya saɓa da dokar kasa, kuma mummunan laifi ne, a don haka za mu bi kadin hakƙin mutanen mu da aka kashe a kuma waɗanda aka jikkata, “in ji shi“.
Kabiru Rurum, ya ce a matsayinsa na wakilin mutanen da aka kashe a majalisar Wakilai ta ƙasa, yana kira ga shugaban Najeriya Bola Tinubu, da babban Sifeton ƴan sanda, da su yi duk mai yiyuwa wajen ganin an kamo waɗanda suka yi wannan aika-aikar tare da hukunta su, da kuma biyan diyya ga iyalan waɗanda suka rasu da kula da waɗanda suka jikkata.
“Kasancewar wannan bashi ne na farko da ake samun wasu ɓata gari na tare matafiya akan hanya da basu ji ba basu gani ba su kashe su, a don haka muna fatan wannan karon gwamnati da sauran hukumomin tsaro za su ƙaddamar da ƙwaƙƙwaran bincike don ɗaukae mataki kamar yadda dokar kasa ta tanada, “in ji Rurum”.
Ɗan majalisar ya kuma jajantawa dukkanin al’ummar jihar Kano musamman Iyalan waɗanda suka rasu, tare da addu’ar Allah ya gafarta musu yasa Jannatul Firdausi makomar su, su kuma waɗanda suka jikkata Allah ya basu lafiya.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su