Connect with us

Wasanni

Kungiyar Bournemouth ta sayi dan wasan kasar Ghana Semenyo

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Bournemouth da ke kasar Ingila, ta sanar da sayan dan wasan gaban kasar Ghana da ke buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Bristol City wato Antoine Semenyo akan kudi yuro miliyan tara.

Semenyo mai shekaru 23, ya rattaba kwantaragin shekaru hudu da rabi da kungiyar kwallon kafa ta Bournemouth, tare da yarjejeniyar kara kwantaraginsa da kungiyar a nan gaba.

Antoine Semenyo na daya daga cikin ‘yan wasan da kasar Ghana ta je da su wasan gasar cin kofin duniya na shekarar 2022 da kasar Qatar ta karbi bakwanci, ya kuma zurawa kungiyar kwallon kafa ta Bristol City kwallaye 21 a wasanni 125 da ya buga mata.

Yanzu haka dai Antoine Semenyo shine dan wasa na uku da Bournemouth ta saya a watan janairun nan da muke ciki, da suka hadar da mai tsaron raga Darren Randolph da Dango Ouattara sai kuma Antoine Semenyo.

Wasanni

Kungiyar Al-Ittihad ta sallami mai horaswar ta Nuno.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Al-Ittihad da ke kasar Saudiyyah ta sallami mai horaswar ta Nuno Espirito Santo, bayan kwashe watanni 16 ya na horas da ita.

Santo dan asalin kasan Portugal mai shekaru 49, kuma tsohon mai horas da Kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Hotspur ta kasar Ingila, ya fara horas da kungiyar Al-Ittihad ne a watan Yuli na shekarar 2022 bayan korar sa da kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Hotspur ta yi.

Kungiyar kwallon kafa ta Al-Ittihad dai ta bayyana cewar ta sallami Nuno Espirito Santo ne sakamakon rashin kokari da kungiyar ta ke yi karkashin jagorancin sa, Al-Ittihad dai tayi nasara ne a wasanni 6 cikin wasanni 12 da ta buga a kakar bana.

A ranar Litinin din da ta gabata ne, Kungiyar kwallon kafa ta Air Force ta kasar Iraq, ta doke Al-Ittihad da ci 2 – 0 a wasan zakarun Asian Champions league.

Continue Reading

Wasanni

Kano Pillars ta koma mataki na hudu a gasar NPFL.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta koma mataki na hudu a gasar cin kofin kwararru na Nigerian

Pillar dai ta doke Kungiyar kwallon kafa ta Bayelsa United ne, da ci uku babu ko daya a wasan mako na shida na gasar ta shekarar 2023 zuwa 2024.

A ranar lahadi 5/11/2023 ne kungiyar ta Kano Pillars za ta ziyarci Kungiyar kwallon kafa ta Sporting Lagos a Jihar Lagos a wasan mako na bakwai na gasar.

Continue Reading

Wasanni

Sakamakon wasan mako na hudu na gasar NPFL

Published

on

Sakamakon wasan mako na hudu na gasar cin kofin kwararru na Najeriya na kakar 2023/2024 wato NPFL.

Tun a ranar Asabar din da ta gaba ta ne 21 Oktoba 2023, aka buga wasa daya tilo kamar haka÷

Niger Tornadoes 1 – 0 Bayelsa United

Sai dai an dage wasa tsakanin kungiyar kwallon kafa ta Doma United da Enyimba

Wasanni da aka buga a ranar Lahadi 22 Oktoba 2023 kuwa÷

Gombe United 1 – 0 Bendel Insurance

Akwa United 0 – 0 Shooting Stars

Heartland Owerri 1 – 1 Katsina United

Kano Pillars 1 – 0 Rivers United

Kwara United 1 – 1 Enugu Rangers

Lobi Stars 2 – 0 Abia Warriors

Plateau United 1 – 0 Sunshine Stars

Remo Stars 2 – 1 Sporting Lagos.

Continue Reading

Trending