Connect with us

Labarai

Matasa ku kauce wa tayar da tarzoma yayin zaɓen 2023 – KAMYA

Published

on

Shugaban ƙungiyar matasa Musulmi ta ƙasa reshen jihar Kano KAMYA, Kwamared Imam Muntaƙa Abdulmalik, ya shawarci matasa da su kaucewa tayar da tarzoma a yayin zaɓen 2023 dake tafe, don gujewa faɗawa komar jami’an tsaro.

Imam Muntaƙa ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwar da ya fitar mai ɗauke da sa hannunsa ya aikowa Dala FM a yau juma’a, inda ya kuma shawarci al’umma musamman ma mata, da su guji siyar da ƙuri’un su domin tamkar siyar da ƴan ci ne.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, Imam Muntaƙa ya kuma yi kira ga al’umma da su baiwa jami’an tsaro haɗin kan da ya dace, musamman ma a yayin zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisun tarayya da za’ayi a gobe Asabar, domin gudanar da aikin cikin nasara.

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.



Continue Reading

Labarai

Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta

Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.

 

Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.



Continue Reading

Daurin Boye

Zan shiga kawancen ‘yan jamiyyar hamayya – tsohon Minista

Published

on

Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan jamiyyar hamayya domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027

A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar.

Amaechi wanda ɗan jam’iyyar APC ne  ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira halin ƙuncin rayuwa da ƙasar ke ciki.

Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance.



Continue Reading

Trending