Connect with us

Labarai

Huɗuba: Kada mu zamo sanadin mutuwar mutum saboda son mulki – Limamin Bachirawa

Published

on

Limamin masallacin juma’a na Jami’ul Rasul dake unguwar Bachirawa Madina, kwanar Madugu Alƙali Mallam Umar Sunusi Ɗan Baba, ya ce, bai kamata saboda neman wani shugabancin siyasa mutum ya ce zai iya yin komai ba, ko da kuwa kashe ran ɗan uwansa ne, saboda tsananin son ɗarewa karagar mulkin.

Alƙali Umar Sunusi mai laƙabin Mallam Abba, ya bayyana hakan ne ta cikin huɗubar Juma’ar da ya jagoranta, a cikin masallacin.

Ya ce, kamata ya yi al’ummar musulmi su ƙara gyara zukatansu domin rabauta da rahamar Allah S.W.T a nan duniya dama gobe ƙiyama.

Malamin ya kuma ce, duk wanda ya kashe rai shima hukuncin kisa ne a kansa a mahanga ta addinin Musulunci.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, Alƙali Umar Sunusi Ɗan Baba ya kuma ƙara da cewa, tsantsar jahilci da zubar da jinin mutane da sauransu na daga cikin alamun tashin Alƙiyama, a don haka al’umma su tashi tsaye wajen neman ilmi.

Labarai

Mu yawaita karanta Alƙur’ani da aikin alkhairi a watan Ramadan – Malam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallaacin Juma’a na Salafussalih dake unguwar Ɗorayi ƙarama Malam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’ummar musulmi da su ƙara himma wajen karanta Al-ƙur’ani mai girma, tare da aikata ayyukan alkhairi domin rabauta da rahamar Allah S.W.T a nan duniya dama gobe ƙiyama.

Mallam Ibrahim Bunkure ya bayyana hakan ne lokacin da yake tsokaci kan huɗubar Juma’ar da ya gabatar yau a masallacin.

Ya ce, kamata yayi musulmai su ƙara yin koyi da kyawawan ɗabi’un Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama, domin zama ababen koyi a rayuwa.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya kuma shawarci al’umma da su ƙara kasancewa masu yafiya musamman a lokacin da aka yi mutu abinda bai musu daɗi ba, bisa mahimmancin da hakan yake da shi.

Continue Reading

Labarai

Marayu na buƙatar tallafi sosai – Kwamared Abu Saleem

Published

on

Shugaban ƙungiyar tallafawa Marayu da ci gaban al’umma ta ƙaramar hukumar Birnin Kano Kwamared Adam Umar Abu Saleem, ya ce ƙarancin samun tallafi daga masu ƙarfi ne ke sanyawa Marayu ke faɗawa cikin mawuyacin hali.

Kwamared Adam Abu Saleem na wannan jawabin ne yayin zantawarsa da gidan rediyon Dala FM, lokacin musabaƙar Alƙur’ani mai girma na marayu ƴan ƙaramar hukumar Birni 5 yayin da ɗalibi dake Karkasara Ja’afar Aliyu Abubakar ya zama gwarzon shekara na ƙaramar hukumar wanda aka ɗauki nauyin al’amuran rayuwarsa baya ga kyaututtuka da ya samu, wanda Musabaƙar ta gudana cikin Firamen Salanta a ranar Asabar.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa Kwamared Adam ya ce sukan shirya Musaɓakar ne domin zaburar da Marayu akan harkokin karatun Alkur’ani mai girma, da kuma rage musu wani tunanin maraici da suke kasancewa a maban-banta lokuta.

Continue Reading

Labarai

Lokacin zaɓe: Rundunar ƴan sanda ta shirya daƙile tayar da tarzoma – SP Kiyawa

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce, ta shirya wajen samar da tsaro, tare da ɗaukar matakin da ya dace ga ɓata garin da suke shirin tayar da tarzoma.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ƴan sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ga Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u a yau juma’a, yayin da yake tsokaci kan shirin da rundunar su ta yi kan zaɓe.

Continue Reading

Trending