Connect with us

Manyan Labarai

Zaben Kano – APC ta gabatar da bukatun ta gaban kotu

Published

on

Jam’iyyar APC reshen Kano ta shigar da kara a gaban kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Kano, tana kalubalantar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kan ayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben da aka gudanar a jihar a ranar 18 ga watan Maris, 2023.

A karar da jam’iyyar APC ta shigar da yammacin ranar Lahadin data gabata, APC na zargin cewa, Abba Kabir Yusuf bai cancanta ya tsaya takara ba, saboda ba ya cikin jerin sunayen mambobin NNPP da aka aika wa hukumar INEC.

Jam’iyyar APC ta kuma yi zargin cewa NNPP ba ta ci zabe da mafi yawan kuri’u na halal ba, tana mai cewa wasu kuri’un da aka kada musu na Jabu ne, kuma idan aka cire su daga kuri’un da NNPPn ta samu, APC ce za ta samu kuri’u ma fi yawa da aka kada.

APC ta kuma yi zargin cewa Baturen Zaben Gwamnan kano ya yi kuskure kan ayyana Abba Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben, inda ta ce tazarar kuri’un da aka samu bai wuce kuri’un da aka soke ba, kamar yadda ta bayyana cewa ya kamata a ce zaben bai kammala ba.

Kazalika APC na bukatar kotun da ta bayyana cewa NNPP ba ta da dan takara saboda Abba Kabir Yusuf baya cikin rajistar masu kada kuri’a da suka mika wa INEC a lokacin zabe, inda ya bukaci kotu ta bayyana Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben, ko kuma ta bayyana APC a matsayin wadda ta lashe zaben da samun mafi yawan kuri’un da aka kada idan an cire kuri’un da APCn tayi zargin na bogi ne da aka kadawa NNPP.

Haka kuma mai shigar da kara ta roki Kotun da ta bayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba, yana mai zargin cewa tazarar ba ta kai adadin kuri’un da aka soke ba.

Tun abaya dai an jiyo jam’iyyar APC na kalubalantar nasarar Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP, inda tace za ta nemi hakkin ta a kotu.

Manyan Labarai

Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Published

on

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.

Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a

“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.

Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.

Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Continue Reading

Manyan Labarai

An ga watan ƙaramar Sallah a Najeriya – Sarkin Musulmi

Published

on

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na uku ya tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya, inda za a yi karamar Sallah gobe Lahadi.

Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a yayin jawabin da ya gabatar a cikin daren Asabar ɗin nan, ya ce sun samu rahotannin ganin watan ne daga sassa daban-daban na ƙasar nan.

Alhaji Sa’ad Abubakar ya ce daga cikin guraren da aiko musu da ganin jinjirin watan na Shawwal akwai Zazzau, da kuma daga Sarkin Dutse, da Arugungu, da kuma Shehun Borno, da dai sauran gurare daban-daban na Najeriya.

Ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su gabatar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali, tare da taimaka wa mabuƙata.

Tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewa, biyo bayan sanarwar fadar mai alfarma Sarkin Musulmi, ya kasance ranar Lahadi take 1 ga watan Shawwal na shekarar 1446, wato ranar ƙaramar Sallah.

Continue Reading

Manyan Labarai

Shugaba Tinubu da Sifeton Ƴan Sanda ku bi wa mutanen mu da aka yi wa kisan gilla hakƙin su – Rt. Hon. Rurum

Published

on

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Rabo, Kibiya da Bunkure, Kabiru Alhassan Rurum, ya bayyana kaɗuwar sa bisa kisan gillan da aka yi wa wasu Mafarauta su kusan 16, a garin Uromi da ke jihar Edo, a lokacin da suke hanyar su ta komawa Kano daga jihar Rivers.

Honarable Kabiru Rurum, ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da aka aikowa Dala FM Kano a ranar Asabar, ya ce daga cikin mutanen da aka ƙona akwai mutum 11 da suka fito daga mazaɓun yankin sa na Kibiya da Bunkure, inda wasu 6 suka samu muggan raunuka suna karɓar Magani yanzu haka a jihar Edo.

A cewar Ɗan Majalisar, “Wannan abu da matasan garin Uromi a jihar Edo, suka yi ya saɓa da dokar kasa, kuma mummunan laifi ne, a don haka za mu bi kadin hakƙin mutanen mu da aka kashe a kuma waɗanda aka jikkata, “in ji shi“.

Kabiru Rurum, ya ce a matsayinsa na wakilin mutanen da aka kashe a majalisar Wakilai ta ƙasa, yana kira ga shugaban Najeriya Bola Tinubu, da babban Sifeton ƴan sanda, da su yi duk mai yiyuwa wajen ganin an kamo waɗanda suka yi wannan aika-aikar tare da hukunta su, da kuma biyan diyya ga iyalan waɗanda suka rasu da kula da waɗanda suka jikkata.

“Kasancewar wannan bashi ne na farko da ake samun wasu ɓata gari na tare matafiya akan hanya da basu ji ba basu gani ba su kashe su, a don haka muna fatan wannan karon gwamnati da sauran hukumomin tsaro za su ƙaddamar da ƙwaƙƙwaran bincike don ɗaukae mataki kamar yadda dokar kasa ta tanada, “in ji Rurum”.

Ɗan majalisar ya kuma jajantawa dukkanin al’ummar jihar Kano musamman Iyalan waɗanda suka rasu, tare da addu’ar Allah ya gafarta musu yasa Jannatul Firdausi makomar su, su kuma waɗanda suka jikkata Allah ya basu lafiya.

Continue Reading

Trending