Connect with us

Manyan Labarai

Zaben Kano – APC ta gabatar da bukatun ta gaban kotu

Published

on

Jam’iyyar APC reshen Kano ta shigar da kara a gaban kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Kano, tana kalubalantar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kan ayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben da aka gudanar a jihar a ranar 18 ga watan Maris, 2023.

A karar da jam’iyyar APC ta shigar da yammacin ranar Lahadin data gabata, APC na zargin cewa, Abba Kabir Yusuf bai cancanta ya tsaya takara ba, saboda ba ya cikin jerin sunayen mambobin NNPP da aka aika wa hukumar INEC.

Jam’iyyar APC ta kuma yi zargin cewa NNPP ba ta ci zabe da mafi yawan kuri’u na halal ba, tana mai cewa wasu kuri’un da aka kada musu na Jabu ne, kuma idan aka cire su daga kuri’un da NNPPn ta samu, APC ce za ta samu kuri’u ma fi yawa da aka kada.

APC ta kuma yi zargin cewa Baturen Zaben Gwamnan kano ya yi kuskure kan ayyana Abba Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben, inda ta ce tazarar kuri’un da aka samu bai wuce kuri’un da aka soke ba, kamar yadda ta bayyana cewa ya kamata a ce zaben bai kammala ba.

Kazalika APC na bukatar kotun da ta bayyana cewa NNPP ba ta da dan takara saboda Abba Kabir Yusuf baya cikin rajistar masu kada kuri’a da suka mika wa INEC a lokacin zabe, inda ya bukaci kotu ta bayyana Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben, ko kuma ta bayyana APC a matsayin wadda ta lashe zaben da samun mafi yawan kuri’un da aka kada idan an cire kuri’un da APCn tayi zargin na bogi ne da aka kadawa NNPP.

Haka kuma mai shigar da kara ta roki Kotun da ta bayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba, yana mai zargin cewa tazarar ba ta kai adadin kuri’un da aka soke ba.

Tun abaya dai an jiyo jam’iyyar APC na kalubalantar nasarar Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP, inda tace za ta nemi hakkin ta a kotu.

Manyan Labarai

APC ta dakatar da Dakta Abdullahi Ganduje daga jam’iyyar

Published

on

Jam’iyyar APC ta dakatar da tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban jam’iyyar na kasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje daga jam’iyyar.

Mai bai wa jam’iyyar shawara a ɓangaren shari’a a mazaɓar Ganduje, da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, Halliru Gwanzo, ya bayyana hakan ne a zantawar sa da manema labarai a jihar ta Kano, kamar yadda jaridar online ta Nigerian Triker ta rawaito.

Halliru Gwanzo, ya kuma ce sun ɗauki matakin dakatar da tsohon gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ne sakamakon zarge-zargen da gwamnatin jihar Kano take masa a kan yin badaƙala da kuɗin al’ummar jahar.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gwamnan Kano ya yi alƙawarin gyara titin garin Kundila da ke ƙaramar hukumar Shanono

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta yi alkawari gyara titin da ya taso daga babban titin karamar hukumar Shanono zuwa garin Kundila da ke karamar hukumar.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ne ya bayyana hakan yayin ta’aziyyar da ya kai na rasuwar ɗan majalisar dokokin jiha mai wakiltar ƙananan hukumomin Ɓagwai da Shanono Honorable Halilu Ibrahim Kundila.

Marigayin dai ya rasu ne a makon da ya gabata.

Gwamna Abba Kabir Yusif ya kuma bayyana kaɗuwar sa a lokacin da yaji rasuwar Marigayin, inda ya ce mutum ne mai gaskiya da rukon amana.

Wakilinmu na fadar gwamnatin jihar Kano Abba Haruna Idris ya rawaito cewa, Abba Kabir ya kuma ce gwamnatin Jihar Kano za ta dauki nauyin karatun iyalan mamacin daga inda suka tsaya har su kammala karatun nasu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Fitacciyar Jarumar Kannywood Saratu Giɗaɗo (Daso) ta rasu

Published

on

Fitacciyar Jaruma a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood Saratu Gidaɗo wadda akafi sani da Daso, ta rasu a yau Talata.

Mijin ƙanwar marigayiya Daso, kuma mai baiwa gwamnan Kano shawara a kan harkokin tafiye-tafiye da shaƙatawa Mustapha Ibrahim Chidari, ne ya tabbatar wa wakilinmu Bashir Sharfaɗi rasuwar ta a ranar Talata.

Ya ce da Asubar yau tayi Sahur, ta koma Bacci, sai dai kuma zuwa wajen ƙarfe 10 na safe aka ga bata fito daga ɗakin ta ba, ko da aka shiga ɗakin ne aka tarar ta rasu.

Mustapha, ya ce za’a yi jana’izar ta da yammacin Talatar nan, da misalin ƙarfe 04:30 a gidanta dake Chiranchi cikin garin Kano.

Marigayiya Daso, guda ce daga cikin fitattun jarumai a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, wadda ta shafe shekaru a masana’antar.

Continue Reading

Trending