Connect with us

Labarai

Za mu bai wa ɗaurarru aikin koyarwa – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, za ta bawa ɗaurarrun da suka kammala karatu aikin koyarwa, domin bunƙasa ilimin su.

Kwamishinan ilmin jihar, Umar Haruna Doguwa ya bayyana hakan, lokacin bikin ta ya murna ga daliban 48 da suka kammala karatun sakandare, a makarantar Iinmate continue education center da ke gidan gyaran hali na Kurmawa a nan Kano.

Ya ce, nan ba da dadewa ba, gwamnati za ta samar da kwamitin yiwa daurarru afuwa, wanda a ciki in dai akwai waɗanda suka cancanta za su iya samun aikin.

Daga bisani kwamishinan ya yi alkawarin bada kowacce irin gudunmawar gwamnati, domin tallafar harkar koyo da koyarwar gidan gyaran halin.

A nasa jawabin, shugaban gidajen ajiya da gyaran hali na jihar Kano, Sulaiman Muhammad Inuwa, ya ce, akwai buƙatar gwamnati da masu hannu da shuni su taimaka wa harkar karatun gidan gyaran halin, domin ganin an sami al’umma ta gari.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….



Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 



Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.



Continue Reading

Trending