Manyan Labarai
Sheikh Giro Argungun ya rasu

Manyan Labarai
Daba a Kano: Mun kama matasa 51 a cikin kwanaki uku – Ƴan Sanda

A ƙoƙarin ta na magance harkokin faɗan Daba da fashin Waya, rundunar Ƴan Sandan jihar Kano, ta kama Matasa 51, cikin kwanaki uku a birnin jihar, tare da samun da muggan Makamai da kuma kayan maye.
A cikin sanarwar da mataimakin kakakin rundunar ƴan sandan jihar DSP Hussain Abdullahi, ya fitar a cikin daren Litinin, ta ce an kama matasan ne a ƙananan hukumomin ƙwaryar birnin Kano, irin su Tarauni, da Gwale, da Dala, Kano Municipal, a cikin unguwannin Zage, Ƙofar Mata, Kurna, da Rijiyar Lemo, Hotoro, da Sheka.
Rundunar ƴan sandan ta kuma ce ba za ta lamunci yadda wasu matasa ke amfani da makamai yayin kiɗan Gangi, lamarin da a wasu lokutan ake ɗaukar su a bidiyo, ko Hotuna riƙe da makamai ana yaɗawa a shafukan Tik-Tok, Facebook, X, da Instagram, da sauran su, abinda ke ƙarawa masu faɗan daban ƙwarin gwiwa akan lamarin.
Cikin sanarwar, Kwamishinan ƴan sandan jihar Kano Ibrahim Adamu Bakori, ya kuma buƙaci iyaye da su ƙara bibiyar al’amuran ƴaƴan su, tare da ɗaukar matakan da suka dace da zarar sun ga halayyar ƴaƴan nasu ta fara canzawa.
A cewar sanarwar, duk wanda ya ga faruwar wani abu da ka iya kawo matsalar tsaro zai iya kiran waɗannan lambobin wayar domin bada bayanan sirri, akan 08032600299, ko 08032600300, ko kuma 08032600301.
Rundunar ta kuma nuna jin daɗin ta bisa haɗin kan da take samu daga ɓangaren al’umma, a ƙoƙarin su na tabbatar da tsaro da zaman lafiya a faɗin jihar Kano.
Kwamishinan ƴan sandan na jihar Kano Ibrahim Bakori, ya kuma bada umarnin fara wasu ayyuka na ba sani ba sabo, amma fa sai an ɗauka da Hakuri, da ƴan daban, da kuma iyayen da suka bar Makami a Gidansu.
Tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewa, ko a ranar Asabar dai, sai da Kwamishian ƴan sandan Kano ta ƙaddamar da sabbin dabarun daƙile harkokin faɗan Daba da fashin Waya da Makami, da sauran ayyuka, a jihar, bayan ganawar sa da manyan jami’an tsaro.

Manyan Labarai
Mun shirya ɗaukar mataki a kan ƴan siyasar da ke ɗaukar nauyin Ƴan Daba a Kano – Anti-Phone Snaching

Rundunar Tsaro da ke yaki da fadan Daba da fashi da makamin Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye ta Anti-Phone Snaching, a jihar Kano, ta ce ta gano cewar yadda wasu daga cikin ‘Yan Siyasa ke daukar nauyin ‘Yan Daba na daga cikin daga cikin dalilan da ke kara ta’azzarar ayyukan ‘yan daban a sassan jihar.
Kwamandan rundunar a Kano Inuwa Salisu Sharada ne ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Litinin, ya ce yanzu haka sun fara bibiya tare da bincike akan irin matasan da suke damun jama’a da fadan Daba a sassan jihar Kano, don gano ‘Yan siyasar da ke da hannu akan lamarin tare da daukar mataki na gaba.
“Abin takaici ne yadda mafi yawancin masu fadan daban ake samun su kananan yara da ba su wuce shekaru 15 zuwa kasa ba, kuma duk da hakan duk wanda mu ka kama ba za mu saurara masa ba, a don haka ne ma mu ke kira ga iyaye da su tsawatar wa ya’yansu, in ji Inuwa”.
A cewar sa, idan suka kama masu harkar faɗan Daba, mafi yawancin su suna kama faɗin wasu daga cikin ƴan siyasa da suke ɗaukar nauyin su, kuma yanzu haka sun dukufa don gano bakin zaren tare da ɗaukar matakin da ya dace akan dukkan masu hannu kan lamarin.
Tuni dai kwamishinan ‘Yan sandan jihar Kano Ibrahim Adamu Bakori, ya kaddamar da sabbin dabarun magance harkokin Daba da fashin Waya da kuma shaye-shayen kayan maye a sassan jihar, bayan da ya gana da manyan jami’an ‘yan sandan a ranar Asabar din da ta gabata.

Manyan Labarai
Kwamishinan Ƴan sandan Kano ya ƙaddamar da sabbin matakan daƙile Daba da Fashin Waya a jihar

Rundunar Ƴan sandan jihar Kano ta sha alwashin kakkaɓe matsalar faɗab Daba, da fashin waya da makami, da Shaye-shayen kayan maye, da ke addabar jama’a a birnin jihar, don wanzar da zaman lafiya.
Kakakin rundunar ƴan Sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikewa manema labarai tashar Dala FM ta samu a ranar Lahadi 15 ga watan Yunin 2025.
Kiyawa, ya ce hakan na zuwa ne bayan da kwamishinan ƴan sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya ƙaddamar da sabbin matakan daƙile ayyukan ’yan daba da masu fashin waya da makami a birnin Kano da kewaye.
Sanarwar ta bayyana cewa kwamishinan ya gana da manyan jami’an rundunar ne a ranar Asabar 14 ga watan Yunin 2025, inda ya umarce su da su soma sumame a dukkan maɓoyar Ƴan Daba, tare da haɗin gwiwa da shugabannin al’umma domin ganin an cafko duk masu hannu a tashe-tashen hankula a faɗin jihar.
“A umarnin da kwamishinan ya bayar, ya umarci dukkanin Baturen Ƴan Sanda wato DPO’s, da shugabannin shiyya na Ƴan Sanda, da sauran dakarun Ƴan sanda, da su nemi haɗin kai da al’umma, tare da ƙara faɗaɗa sintiri don magance matsalolin Daba, da fashin Waya a Kano, in ji Kiyawa”
Har ila yau, rundunar ƴan sandan ta kuma buƙaci haɗin kan jama’a da su rika bayar da bayanan sirri a kan yan daban, ta hanyar kiran waɗannan lambobin wayar 08032419752, ko 08123821575, 09029292926.

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su