Hangen Dala
Majalisa ta dakatar da Shugaban karamar hukumar Gwale

Majalisar dokokin jihar Kano, ta dakatar da shugaban ƙaramar hukumar Gwale Khalid Ishaq Diso na tsawon watanni uku.
Majalisar ta ɗauki matakin ne a zamanta na yau Talata bayan samunsa da laifin sayar da wuraren gwamnati ba bisa ƙa’ida ba.
Majalisar ta kuma ce ta same shi da laifin rashin gudanar da aiki da majalisar kansilolin karamar hukumar da sauran wasu laifukan.
Hakan ya biyo bayan rahoton bincike kan ƙofin da aka gabatar wa majalisar a kansa.
Majalisar ta kuma sanar da maye gurbin Khalid Ishaq Diso da mataimakinsa tsahon watanni uku har sai an kammala bincike.
A ganawarsa da manema labarai, shugaban kwamitin harkokin Ƙananan hukumomi da masarautu kuma ɗan kuma wakilin Sumaila a zauren Alhaji Zubairu Hamza Massu, ya bayyana rahoton da kwamitin nasu ya gabatar.

Baba Suda
NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.
Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.
A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.
Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Daurin Boye
Zan shiga kawancen ‘yan jamiyyar hamayya – tsohon Minista

Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan jamiyyar hamayya domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027
A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar.
Amaechi wanda ɗan jam’iyyar APC ne ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira halin ƙuncin rayuwa da ƙasar ke ciki.
Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance.

Baba Suda
Dumamar yanayi :- Gwamna Zulum ya haramta sare bishiyu

Gwamnan jihar Borno Baba Gana Umar Zulum ya kaddamar da wasu dokokin biyu ga al’ummar Jihar.
Dokar farko itace Gwamnan ya haramta sare bishiyu a dukkanin fadin jihar, Inda kuma ya Kara kaddamar da dokar tsaftace muhalli a dukkanin karshen wata.
Yayin da yake kaddamar da dokar Gwamna Zulum yace duba da dumamar yanayi da ake fuskanta a yanzu gwamnati ta haramta sare bishiyu a fadin jihar Borno.
Haka kuma saboda Kare lafiya da kuma al’ummar Jihar dole ne dukkanin karshen wata a gudanar da tsaftar muhalli a Jihar Borno.
” A matsayi na Wanda kundin tsarin mulkin kasa ya bani dama, ni Baba Gana Umara Zulum na haramta sare bishiyu a fadin jihar Borno, kuma na saka dokar wajibi ne kowa ne dan Jihar ya tsaftace muhalli a dukkanin karshen wata, saboda inganta lafiyar al’ummar Jihar Borno.”

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su