Connect with us

Labarai

Za mu daƙile tayar da hargitsi yayin yanke hukuncin zaɓen gwamna- Civil Defence

Published

on

Rundunar tsaro da bayar da kariya ga al’umma ta Civil Defence da ke jihar Kano, ta ce, za ta gudanar da aikin ba sani ba sabo a kan dukkanin waɗanda suka nemi tayar da hargitsi a gobe Laraba, yayin yanke hukuncin zaɓen gwamna a jihar.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar DSC Ibrahim Idris Abdullahi ne, ya bayyana hakan, yayin zantawarsa da gidan rediyon Dala FM a ranar Laraba, lokacin da yake tsokaci kan haɗin kan da za su yi da sauran rukunin jami’an tsaro kan tsaron da za su bayar yayin yanke hukuncin da Kotun karɓar ƙorafe-korafen zaɓen gwamna za tayi a gobe Laraba.

Ya ce, “Ba za su saurarawa duk wanda ya nemi tayar da hargitsin ba”.

Wakilnmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar, DSC Ibrahim Idris ya kuma yi kira ga shugabannin al’umma, da su ka haɗar da masu riƙe da masarautun gargajiya, malamai da sauransu da su ci gaba da wayar da kan mutane domin ganin an samu zaman lafiya da cigaba.

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.



Continue Reading

Labarai

Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta

Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.

 

Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.



Continue Reading

Daurin Boye

Zan shiga kawancen ‘yan jamiyyar hamayya – tsohon Minista

Published

on

Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan jamiyyar hamayya domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027

A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar.

Amaechi wanda ɗan jam’iyyar APC ne  ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira halin ƙuncin rayuwa da ƙasar ke ciki.

Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance.



Continue Reading

Trending