Connect with us

Hangen Dala

Jawabin Atiku na yau litinin

Published

on

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya nemi gaggauta yi wa tsarin mulkin kasar gyaran fuska don hana duk wata kotu abin da ya kira “boyewa a bayan ka’idojin shigar da kara da musun karya wajen tabbatar da zaben sata da kuma yin zagon kasa ga zaben al’umma”.

 

Atiku Abubakar ya kuma ce dole ne a mayar da zabe da tattara sakamakon zabe ta hanyar laturoni su zama tilas a Najeriya.

 

Wannan wani bangare ne na taron manema labarai da shugaban adawar, kuma dan takarar jam’iyyar PDP a zaben 2023, ya gabatar ranar Litinin a Abuja. Taron na zuwa ne kwana uku bayan hukuncin kotun koli da ta yi watsi da shari’arsa na kalubalantar nasarar shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu.

 

Atiku ya ce matsayin Kotun Koli ko da yake, shi ne karshe amma dai ya bar baya da kura mai yawa.

 

 

Jagoran adawar na Najeriya ya bukaci bullo da tsarin wa’adin mulki daya na tsawon shekara shida kawai a kasar, wanda ya ce zai riga zagayawa tsakanin shiyyoyin Najeriya guda shida.

 

A cewarsa, hakan zai rage neman mulki ido rufe daga shugabannin da ke kan karagar mulki da kuma raba musu hankali.

 

Sannan matakin a cewar Atiku zai inganta tsarin raba daidai da kuma hadin kan kasa a Najeriya.

 

Haka kuma zai hana wasu shiyyoyi guda biyu ko fiye yin taron dangi suna musayar kujerar shugaban kasa a tsakaninsu ta hanyar mayar da sauran saniyar ware.

 

Karin shawarwarin da Atiku Abubakar ya bayar su ne dora wa hukumar zabe ta Najeriya, alhakin tantance takardun da ‘yan takara da jam’iyyunsu suka gabatar, kuma idan ta gaza yin haka, mai yiwuwa saboda hukumomin da aikin ya rataya a wuyansu ba su yi ba, wajibi ne ta bayyana wa jama’a.

 

Atiku ya ce shawarar na cikin muhimman gyaran fuska da aka gabatar wa gwamnatin mulkin soja wadda ta shirya Babban Taron Tsarin Mulki na Kasa kafin mayar da Najeriya kan tafarkin dimokradiyya.

 

Atiku Abubakar ya ce ba zai taba ja da baya a kan gwagwarmayar da ya faro ba.

 

Ya ce matukar yana raye zai ci gaba da gwagwarmaya tare da ‘yan Najeriya a kan “kyautata dimokradiyyarmu da tsarin aiki da doka da kuma sake fasalin siyasa da tattalin arziki” da Najeriya ke bukata don cimma hakikanin bunkasar arzikinta.

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Hangen Dala

Gaya Ajingi Albasu:- Dan majalisa ya raba kayan abinci

Published

on

Dan majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu Dakta Ghali Mustafa Fanda ya fara rabon tallafin kayan abinci ga al’ummar kananan hukumomin uku.

 

Yayin rabon tallafin kayan abincin, Dakta Ghali Mustafa yace yayi rabon tallafin ne domin fara sauke nauyin al’ummar da yake wakilta.

 

” Wannan tallafi zamu bayar da shi ne domin fara sauke nauyin al’ummar da suka zabe mu, kuma wannan shi ne karon farko, kuma yayi daidai da bukatar al’umma a yanzu, shiyasa muka fara da tallafin kayan abinci”.

 

“A cikin wannan tallafi mutane kimanin dubu ashirin ne zasu amfana, wanda zamu bayar da buhunan Shinkafa da Gero da Garin masara.”

 

Haka kuma ɗan majalisar ya bayar da tallafin Naira miliyan ashirin ga matasan kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu.

 

Sai kuma ɓangaren dalibai mata, wanda shima a yau dan majalisar ya dauki nauyin karatun dalibai mata guda 60 a bangaren lafiya.

 

Haka kuma cikin jawabin nasa Hon Ghali ya kuma ce nan gaba kadan zai bayar da tallafin taki ga manoma, da kuma farfaɗo da dukkanin rijiyon burtsatse na kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu a wani mataki na samar da ruwan sha.

 

Da yake nasa jawabin mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam Gwarzo wanda ya samu wakilcin mai baiwa Gwamna Shawara kan harkokin siyasa Hon Sunusi Surajo Kwankwaso kira yayi ga sauran wakilan al’umma da suyi koyi da Dakta Ghali Mustafa Fanda wajen ayyukan alkhairi da kuma jin kan al’umma.

 

Haka kuma Hon Sunusi Surajo ya yabawa dan majalisar bisa bayar da tallafin ga ƙananan hukumomin uku.

 

Taron dai wanda ya gudana a cikin Islamic Centre na karamar hukumar Gaya ya samu halartar manya, da kuma jagororin yankunan uku, kuma nan take Dan majalisar Tarayya Dakta Ghali Mustafa ya fara rabon tallafin

Continue Reading

Hangen Dala

Shugaban kasa ya bayar da umarnin bude Boda

Published

on

Shugaban kasa Asuwaju Bola Ahmad Tinubu ya bayar da umarnin bude iyakokin kasar nan.

Cikin sanarwar da ya fitar shugaban ya ce duk wata iyaka dake tsakanin Nigeria da jamhuriyar Nijar a gaggauta bude ta.

Karin bayani na nan tafe…

Continue Reading

Trending