Connect with us

Addini

Hada masabakar Al-kur’ani na habaka ilimin addinin Musulunci – Sarkin Musulmi

Published

on

Mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya bukaci Musulmi da su ci gaba da dabbaka gasar karatun Al-Kur’ani mai girma, bisa yadda gasar ke karfafa haddar Alkur’ani a fadin Duniya.

Sarkin Musulmi, wanda Shehun Borno Abubakar Ibn Umar Garbai Al-Amin Ibn El-kanemi ya wakilta, ya bayyana hakan ne a wajen taron kaddamar da Musabakar karatun Al-Kur’ani ta Kasa Karo na 38, dake gudana a Damaturun jihar Yobe.

Ya kuma yabawa gwamnatin Yobe bisa daukar nauyi da kuma yadda aka raba bangaren maza da na mata wajen gudanar da gasar.

“Gudanar da masabakar na habaka ilimin addinin Musulunci musamman a tsakanin matasa, inda suke dagewa su yi karatunsa har su zama zakaru a duniyar Musulmi, “in ji Sarkin Musulmi”.

A nasa jawabin maraba a taron da ya gudana a Filin Wasa na 27 Augusta, shugaban kwamitin musabakar, tsohon gwamnan Yobe, Sanata Ibrahim Gaidam, ya yaba wa Jami’ar Usmanu Dan Fodiyo da ke Sakkwato, dangane da kokarinta wajen shirya gasar a matakin kasar nan.

Daga bisani dai ya kuma jinjina wa kwamitocin gasar ta Alkur’ani dangane da yadda suka jajirce wajen ganin an gudanar da ita kamar yadda aka bukata, kamar yadda jaridar Aminiya ta rawaito.

Addini

Matsin Rayuwa: Shugabanni ku sassautawa al’umma – Babban Limamin Kano

Published

on

Babban limamin Kano, kuma wanda ya jagoranci sallar idi a babban masallacin idin na Kofar Mata a nan Kano, Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, ya ja hankalin shugabanni da su sassautawa al’umma, sakamakon halin matsin rayuwar da ake ciki a yanzu.

Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, yayi jan hankalin ne yayin huɗubar da ya gabatar, bayan kammala sallar idi da ta gudana a yau Laraba, a babban masallacin idin dake unguwar Kofar Mata a Kano.

Ya kara da cewa kasancewar al’umma na cikin mawuyacin hali da kuncin rayuwa, akwai buƙatar shugabanni su yi bakin ƙoƙarin su, domin kawo sauki daga halin matsin halin rayuwar da ake fama dashi.

Yayin sallar Idin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da mataimakin sa Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da sauran al’umma da dama ne suka halarta.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito cewa, Farfesa Muhammed Sani ya kuma ja hankalin al’umma, da su koma ga Allah Subhanahu wata’ala domin samun dacewa a Duniya da gobe Ƙiyama.

Continue Reading

Addini

Ku fara duban watan Sallah daga gobe Litinin – Fadar Sarkin Musulmi

Published

on

Yanzu haka kwamitin ganin wata na Fadar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya buƙaci al’ummar musulmin ƙasar nan da su fara duban jinjirin watan Shawwal, daga gobe Litinin, 8 ga watan Afrilun, 2024 da ake ciki.

Bayanin hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da kwamitin ya fitar a yammacin yau Lahadi a jihar Sokoto.

Sanarwar ta ce, duk wanda ya ga watan Shawwal, ya sanarwa Mai Gari ko Hakimi mafi kusa wanda kuma zai sanar har zuwa fadar Sarkin Musulmi.

Har ila yau, fadar Sarkin musulmin ta kuma bayar da lambobin waya waɗanda mutane za su yi amfani da su wajen ba da rahoton ganin watan Sallah ga fadar Sarkin musulmin, kamar yadda kafar yaɗa labarai ta BBC ta rawaito.

Continue Reading

Addini

Iyaye ku kula da tarbiyyar ƴaƴan ku – Malama Fatima Tsakuwa

Published

on

Malamar addinin musulunci dake nan Kano Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta shawarci mata da su ƙara himma wajen kula da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da kuma zaburar da su mahimmancin yin addu’a a cikin wannan wata na Ramadana, domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T.

Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta bayyana hakan ne yayin taron bita ta musamman da gidauniyar Bango Charity Foundation ƙarƙashin Malama Fatima Yusif Mai tama, wanda gidauniyar ta shirya wa Mata, da bitar ta shafi watan Azumin Ramadana, akan yadda iyaye matan za su kula da ƴaƴan su, da ya gudana a ofishin ƙungiyar dake unguwar Sharaɗa a Kano.

Wakiliyar tashar Dala FM Kano, ta rawaito cewa malama Fatima Tsakuwa ta ce akwai buƙatar iyayen su ƙara lura da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma domin rabauta da falala a wajen Allah S.W.T.

Continue Reading

Trending