Connect with us

Addini

Samar da darasin hukunce-hukuncen addinin musulunci a makarantun gaba da sakandire zai taimaki dalibai – Prof. Bashir Aliyu Umar

Published

on

Limamin masallacin juma’a na Alfurkan dake nan Kano Farfesa Bashir Aliyu Umar, ya shawarci masu ruwa da tsaki da su samar da wani fanni da za’a rinka koyar da dalibai masu koyon aikin lafiya hukunce-hukuncen addinin muaukunci a cikin makarantun gaba da sakandire da na koyar da harkar lafiya, bisa mahimmancin da hakan ke da shi ga al’ummar musulmi.

Limamin ya bayyana hakan ne ta bakin wakilicin da ya samu na Daraktan gidauniyar Alfurkan Charity Foundation Dakta Abubakar Muhammad Abubakar, yayin taron wayar da kai akan yadda ya kamata ma’aikatan lafiya su kiyaye hukunce-hukuncen addinin musulunci a aikin su.

Kungiyar musulmai masu lura da lafiya Jinya ta kasa IMAN, ne da hadin gwiwa da Kungiyar mata musulmi ta Afrika ta kasa AMWA, suka shirya taron inda aka gudanar a ranar Lahadi.

Ya kuma ce akwai bukatar ma’aikatan lafiyar su kara kiyaye hukunce-hukuncen addinin musulunci yayin gudanar da ayyukansu, musamman ma wajen kula da kwadaitar da marasa lafiya yin ibada ko da kuwa yana cikin tsananin ciwo ne bisa mahimmancin da hakan ke da shi.

Da take nata jawabin shugabar Kungiyar mata musulmi ta Afrika ta kasa AMWA, Aisha Ishak Sulaiman, da shugabar Kungiyar musulmai masu lura da lafiya ta kasa IMAN, Salamatu Ibrahim, sun ce sun shirya taron ne domin wayar da kan ma’aikatan lafiyar a mahanga ta addinin musulunci, domin ganin an gudu tare an kuma tsira tare.

A nata jawabin mukaddashiyar babban kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano a bangaren mata, Hajiya Khadijah Sagir Sulaiman, shawartar ma’aikatan lafiyar ta yi da su kiyaye da dokokin Ubangiji S.W.T, a aikin su.

Yayin taron dai jami’an Jinya, da ma likitoci da sauran al’umma da dama ne suka samu damar halarta daga sassa daban-daban na jihar Kano.

Addini

Ku taimakawa mabuƙata da Naman Sallah bisa halin matsin rayuwar da ake ciki – Limami

Published

on

Babban limamin masallacin juma’a na Alaramma Abubakar Ɗan Tsakuwa, da ke unguwar Ja’en Ring road Mallam Abdulkareem Aliyu, ya yi kira ga al’ummar Musulmi, da su kiyaye ƙa’idojin yanka Dabbobin Layyah, domin gujewa cin mushen Nama.

Mallam Abdulkareem Aliyu, ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u, lokacin da yake tsokacin huɗubar da ya gabatar ranar Sallar Idin da ya jagoranta a masallacin ranar Lahadi 17 ga watan Yunin 2024.

Ya ce a mafi yawan lokuta al’umma sukan yanka dabbobi amma rashin bin ƙa’idojin yanka yakan sanya wa su ci mushen nama ba tare da sun sani ba, a dan haka su tashi tsaye wajen sanin yadda ake yanka Dabbobin a mahanga ta addinin Musulunci.

A cewar sa, “Musulmai ku kwaɗaitu da yin sadakar naman layya musamman ma ga masu ƙaramin ƙarfi domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T, “in ji shi”.

Mallam Abdulkareem Aliyu, ya kuma ce, akwai buƙatar a kiyaye nau’ikan dabbobin da aka sahale ayi layya da su, waɗanda suka haɗar da nau’in Sa ko Saniya, da kuma Raƙumi ko Raƙuma (Taguwar), ko kuma Rago ko Tinkiya, ko Akuya ko kuma Ɗan Akuya.

Wannan dai na zuwa ne bayan da al’ummar Musulmin Duniya suka gudanar da babbar Sallah, a jiya Lahadi 16 ga watan Yunin shekarar 2024.

Continue Reading

Addini

An ga jinjirin watan Zul-Hijjah a Najeriya, ranar Lahadi 16 ga watan Yuni Babbar Sallah

Published

on

Fadar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Abubakar Sa’ad na uku, ta sanar da ganin jinjirin watan Zul-Hijjah na shekarar 1445.

Hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmin ta fitar, mai ɗauke da sa hannun Wazirin Sakkwato, kuma shugaban kwamitin duban wata Farfesa Sambo Wali Junaid.

Sanarwar ta kuma ce duba da ganin jaririn watan na Zul-Hijjah da akayi a jiya Alhamis, hakan ya tabbatar da cewar yau Juma’a ɗaya ga watan Zul-Hijjah, wanda za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan Yunin 2024.

Tun dai a jiya Alhamis hukumomi a ƙasar Saudiyya suka sanar da ganin Jaririn watan na Zul-Hijjah, lamarin da ya kasance za’ayi tsayuwar Arafa a ranar Asabar 15 ga watan Yunin 2024, yayin da za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan na Yuni.

Kafar Dala FM Kano, ta rawaito cewa, kawo yanzu dai maniyyata aikin hajjin bana da dama ne ke ci gaba da shiga ƙasa mai tsarki, a ƙoƙarin su na zuwa domin sauke Farali.

Continue Reading

Addini

Matsin Rayuwa: Shugabanni ku sassautawa al’umma – Babban Limamin Kano

Published

on

Babban limamin Kano, kuma wanda ya jagoranci sallar idi a babban masallacin idin na Kofar Mata a nan Kano, Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, ya ja hankalin shugabanni da su sassautawa al’umma, sakamakon halin matsin rayuwar da ake ciki a yanzu.

Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, yayi jan hankalin ne yayin huɗubar da ya gabatar, bayan kammala sallar idi da ta gudana a yau Laraba, a babban masallacin idin dake unguwar Kofar Mata a Kano.

Ya kara da cewa kasancewar al’umma na cikin mawuyacin hali da kuncin rayuwa, akwai buƙatar shugabanni su yi bakin ƙoƙarin su, domin kawo sauki daga halin matsin halin rayuwar da ake fama dashi.

Yayin sallar Idin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da mataimakin sa Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da sauran al’umma da dama ne suka halarta.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito cewa, Farfesa Muhammed Sani ya kuma ja hankalin al’umma, da su koma ga Allah Subhanahu wata’ala domin samun dacewa a Duniya da gobe Ƙiyama.

Continue Reading

Trending