Connect with us

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Kasar Cote D’Ivoire ta yi nasara akan Najeriya 2-1, a gasar nahiyar Afrika ta Afcon 2023.

Published

on

Kasar Ivory Coast ta lashe gasar cin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) na 2023, bayan doke Najeriya da ci 2 da 1 a wasan karshe na gasar.

Rahotanni dai sun bayyana cewar mai masaukin bakin ta zama zakara ne, bayan ta warware kwallon da Najeriya ta jefa mata kafin tafiya hutun rabin lokaci a raga.

Yayin wasan dai dan wasan bayan Najeriya, Troost Ekoong ne ya fara jefa mata kwallo a minti na 38 a ragar Ivory Coast.

Sai dai kuma bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Ivory Coast ta warware kwallon a minti na 62 ta hannun dan wasan tsakiyarta, Franck Kessie.

Yayin da aka kai munti na 81 Sebastian Haller ya kara wa mai masaukin baki kwallo ta biyu a raga, wanda hakan ya sanya ta zama zakarar AFCON ta 2023.

Yanzu haka dai ana shirye-shiryen bayar da kyauta ga kasar da ta yi nasara, da kuma wadanda aka shirya baiwa kyaututtukan, wanda kuma a wajen yanzu haka akwai mataimakin shugaban kasa Kasheem Shatima, da gwamnan jihar Katsina Umar Dikko Radda, da na jihar Nassarawa Abdullahi Sule, da kuma ministan Wasanni, da sauransu.

Idan ba a manta ba Najeriya ta doke Ivory Coast a wasan rukuni da suka fafata da ci daya ta hannun Troost Ekoong a bugun fanareti, kamar yadda jaridar Aminiya ta rawaito.

Continue Reading

Trending