Connect with us

Addini

Tsadar Rayuwa: Zamu kara kudin makaranta daga yanzu zuwa kowanne lokaci – Kungiyar hadin kan malaman Islamiyya da Tsangayu

Published

on

Kungiyar hadin kan Malaman Makarantun Islamiyya da Tsangayu ta jihar Kano ta yi barazanar yin karin kudin makaranta sakamakon tsadar rayuwar da ake fama da ita a kasa.

Shugaban kungiyar na jihar Kano, kuma limamin masallacin Juma’a na Ikhwanul Musdafha, Malam Kamalu Sa’id Habib Mai Jabbaru, ne ya sanar da hakan yayin zantawarsa da manema labarai a ofishinsa.

Mai Jabbaru ya kuma ce tun kafin zuwan wannan lokaci na tsadar kayayyakin masarufi, ana samun karancin taimakekeniya tsakanin malamai da iyayen dalibai, hakan ya sa suka ga dacewar yin karin kudin makarantar domin ganin ba’a kuntatawa kowa ba.

Ya kuma bayyana mamakinsa bisa yadda wasu daga cikin iyayen daliban ke sawa malamin Islamiyya ko na tsangaya ido a sanda suka ga wani canji a tare da shi, kan abinda ya shafi cinsa da shansa da kuma sitirar da yake sakawa, duk kuwa da kyamatar da wasu ke nunawa na kin aminta da su dauki aure su baiwa malamin Islamiyya.

Daga karshe shugaban Kungiyar Hadin Kan Malaman Makarantun Islamiyyun da Tsangayu, mallam mai Jabbaru ya bukaci Malamai da su kara kudin Makarantar da bai gaza Naira dari ba, musamman ma masu karbar kudin wata ko na Laraba da kuma masu karbar na watanni 3 bisa la’akari da halin da kasar nan take ciki yanzu na tsadar rayuwa da ake ciki.

Addini

Matsin Rayuwa: Shugabanni ku sassautawa al’umma – Babban Limamin Kano

Published

on

Babban limamin Kano, kuma wanda ya jagoranci sallar idi a babban masallacin idin na Kofar Mata a nan Kano, Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, ya ja hankalin shugabanni da su sassautawa al’umma, sakamakon halin matsin rayuwar da ake ciki a yanzu.

Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, yayi jan hankalin ne yayin huɗubar da ya gabatar, bayan kammala sallar idi da ta gudana a yau Laraba, a babban masallacin idin dake unguwar Kofar Mata a Kano.

Ya kara da cewa kasancewar al’umma na cikin mawuyacin hali da kuncin rayuwa, akwai buƙatar shugabanni su yi bakin ƙoƙarin su, domin kawo sauki daga halin matsin halin rayuwar da ake fama dashi.

Yayin sallar Idin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da mataimakin sa Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da sauran al’umma da dama ne suka halarta.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito cewa, Farfesa Muhammed Sani ya kuma ja hankalin al’umma, da su koma ga Allah Subhanahu wata’ala domin samun dacewa a Duniya da gobe Ƙiyama.

Continue Reading

Addini

Ku fara duban watan Sallah daga gobe Litinin – Fadar Sarkin Musulmi

Published

on

Yanzu haka kwamitin ganin wata na Fadar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya buƙaci al’ummar musulmin ƙasar nan da su fara duban jinjirin watan Shawwal, daga gobe Litinin, 8 ga watan Afrilun, 2024 da ake ciki.

Bayanin hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da kwamitin ya fitar a yammacin yau Lahadi a jihar Sokoto.

Sanarwar ta ce, duk wanda ya ga watan Shawwal, ya sanarwa Mai Gari ko Hakimi mafi kusa wanda kuma zai sanar har zuwa fadar Sarkin Musulmi.

Har ila yau, fadar Sarkin musulmin ta kuma bayar da lambobin waya waɗanda mutane za su yi amfani da su wajen ba da rahoton ganin watan Sallah ga fadar Sarkin musulmin, kamar yadda kafar yaɗa labarai ta BBC ta rawaito.

Continue Reading

Addini

Iyaye ku kula da tarbiyyar ƴaƴan ku – Malama Fatima Tsakuwa

Published

on

Malamar addinin musulunci dake nan Kano Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta shawarci mata da su ƙara himma wajen kula da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da kuma zaburar da su mahimmancin yin addu’a a cikin wannan wata na Ramadana, domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T.

Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta bayyana hakan ne yayin taron bita ta musamman da gidauniyar Bango Charity Foundation ƙarƙashin Malama Fatima Yusif Mai tama, wanda gidauniyar ta shirya wa Mata, da bitar ta shafi watan Azumin Ramadana, akan yadda iyaye matan za su kula da ƴaƴan su, da ya gudana a ofishin ƙungiyar dake unguwar Sharaɗa a Kano.

Wakiliyar tashar Dala FM Kano, ta rawaito cewa malama Fatima Tsakuwa ta ce akwai buƙatar iyayen su ƙara lura da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma domin rabauta da falala a wajen Allah S.W.T.

Continue Reading

Trending