Connect with us

Addini

Ku guji ɓatawa iyayen ku rai domin gujewa fushin Allah S.W.T – Mal. Muhktar Faragai

Published

on

Malamin addinin musuluncin nan dake jihar Kano Malam Muhktar Abdullahi Faragai, ya shawarci al’umma da su kasance masu yiwa iyayen su biyayya musamman ma uwa ko da kuwa ta rasu ne bisa mahimmancin da take da shi.

Mallam Muhktar Faragai ya bayyana hakan ne ta cikin shirin Duniya Labari Ce, da ya gudana yau Asabar a tashar Dala FM Kano, ya ce kasancewar Ma’aiki S.A.W. ya umarci a yiwa mahaifiya biyayya har sau uku sannan mahaifi, a dan haka akwai buƙatar ƴaƴa su rinƙa yiwa mahaifiyar su biyayya ba tare da saɓa mata ba.

Ya kuma shawarci iyaye da su kara ƙoƙari wajen sauke nauyin ƴaƴan su da Allah S.w.t. ya ɗora musu, domin ganin rayuwar ƴaƴan ta zama abar koyi a tsakanin al’umma.

“Ku guji ɓatawa iyayen ku rai domin fushin su a kan ku ka iya sanyawa ku fuskanci fushin Allah S.W.T, “in ji Mal. Muhktar”.

Ya ci gaba da cewa, “Matakin farko a biyayya shine yiwa Allah S.W.T, biyayya, da kuma Ma’aiki S.A.W, sannan biyayya ga iyaye, wanda gujewa yin hakan babbar matsala ce ga rayuwar al’umma”.

Malam Muhktar Faragai ya kuma shawarci iyaye da su guji yin fushi da ƴaƴan su, tare da kaucewa riƙe su a cikin zuciyar su saboda sun yi musu wani abu, inda ya ce mai-makon hakan yafi dacewa su yi haƙuri tare da rinƙa yi musu addu’a.

Addini

Matsin Rayuwa: Shugabanni ku sassautawa al’umma – Babban Limamin Kano

Published

on

Babban limamin Kano, kuma wanda ya jagoranci sallar idi a babban masallacin idin na Kofar Mata a nan Kano, Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, ya ja hankalin shugabanni da su sassautawa al’umma, sakamakon halin matsin rayuwar da ake ciki a yanzu.

Farfesa Muhammed Sani Zaharaddin, yayi jan hankalin ne yayin huɗubar da ya gabatar, bayan kammala sallar idi da ta gudana a yau Laraba, a babban masallacin idin dake unguwar Kofar Mata a Kano.

Ya kara da cewa kasancewar al’umma na cikin mawuyacin hali da kuncin rayuwa, akwai buƙatar shugabanni su yi bakin ƙoƙarin su, domin kawo sauki daga halin matsin halin rayuwar da ake fama dashi.

Yayin sallar Idin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da mataimakin sa Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da sauran al’umma da dama ne suka halarta.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito cewa, Farfesa Muhammed Sani ya kuma ja hankalin al’umma, da su koma ga Allah Subhanahu wata’ala domin samun dacewa a Duniya da gobe Ƙiyama.

Continue Reading

Addini

Ku fara duban watan Sallah daga gobe Litinin – Fadar Sarkin Musulmi

Published

on

Yanzu haka kwamitin ganin wata na Fadar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya buƙaci al’ummar musulmin ƙasar nan da su fara duban jinjirin watan Shawwal, daga gobe Litinin, 8 ga watan Afrilun, 2024 da ake ciki.

Bayanin hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da kwamitin ya fitar a yammacin yau Lahadi a jihar Sokoto.

Sanarwar ta ce, duk wanda ya ga watan Shawwal, ya sanarwa Mai Gari ko Hakimi mafi kusa wanda kuma zai sanar har zuwa fadar Sarkin Musulmi.

Har ila yau, fadar Sarkin musulmin ta kuma bayar da lambobin waya waɗanda mutane za su yi amfani da su wajen ba da rahoton ganin watan Sallah ga fadar Sarkin musulmin, kamar yadda kafar yaɗa labarai ta BBC ta rawaito.

Continue Reading

Addini

Iyaye ku kula da tarbiyyar ƴaƴan ku – Malama Fatima Tsakuwa

Published

on

Malamar addinin musulunci dake nan Kano Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta shawarci mata da su ƙara himma wajen kula da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da kuma zaburar da su mahimmancin yin addu’a a cikin wannan wata na Ramadana, domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T.

Malama Fatima Ahmad Tsakuwa, ta bayyana hakan ne yayin taron bita ta musamman da gidauniyar Bango Charity Foundation ƙarƙashin Malama Fatima Yusif Mai tama, wanda gidauniyar ta shirya wa Mata, da bitar ta shafi watan Azumin Ramadana, akan yadda iyaye matan za su kula da ƴaƴan su, da ya gudana a ofishin ƙungiyar dake unguwar Sharaɗa a Kano.

Wakiliyar tashar Dala FM Kano, ta rawaito cewa malama Fatima Tsakuwa ta ce akwai buƙatar iyayen su ƙara lura da tarbiyyar ƴaƴansu, tare da yawaita karatun Al-kur’ani mai girma domin rabauta da falala a wajen Allah S.W.T.

Continue Reading

Trending