Connect with us

Addini

Yanzu yanzu:- Daurawa ya koma mukamin sa

Published

on

Bayan wata ganawa da akayi tsakanin gwamnan Kano da kuma zauren hadin kan malaman jihar karshe an cimma matsayar sheik Aminu Ibrahim Daurawa zai koma kujerar sa ta shugabancin hukumar Hisba.

Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren kungiyar Dakta Sa’idu Ahmad Dukawa yace bayan dogon nazari kungiyar ta fahimci shedan ne ya so shiga tsakanin gwamnan Kano da sheik Malam Aminu Daurawa.

A baya bayan nan ne dai gwamnan Kano injiniya Abba Kabir Yusuf yayi wasu kalamai dake nuna rashin gamsuwa da ayyukan hukumar Hisba wanda kalaman ya sabbaba saukar Malam Daurawa daga mukamin sa.

A daren wannan Litinin dai zauren hadin kan malaman suka yi wannan zama da gwamnan Kano, inda a karshe aka cimma matsayar sulhu kuma nan take Malam Aminu Daurawa ya amince zai cigaba da jagorantar hukumar ta Hisba.

Addini

Hukumar Shari’a ta shirya buɗe baki ga Mutanen da suka musulunta a Kano

Published

on

A ƙoƙarin ta na ƙara ɗaɓɓaƙa harkokin addinin Musulunci, hukumar Shari’ah ta jihar Kano da haɗin guiwar kungiyar World Assembly of Muslim Youth (Wamy), sun shirya wa waɗanda suka karbi addinin Musulunci shan ruwa a ranar Lahadi 23 ga Ramadan shekarar 1446.

Taron shan ruwan dai ya gudana ne a harabar hukumar karkashin Jagorancin Mukaddashin Shugaban ta Sheikh Ali Ɗan Abba.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Muƙaddashin Daraktan yaɗa labarai na hukumar shari’a ta jihar Kano, Musa A Ibrahim (Best Seller).

Hukumar Shari’ar ta kuma ayyana ranar 15 ga Ramadan domin ta zama ranar da za ta rinƙa shan ruwa da waɗanda suka karɓi addinin Musulunci da za a rinƙa yi a duk shekara.

“Muna kuma miƙa godiya ga gwamnatin jihar Kano a karkashin gwamna Abba Kabir Yusuf, da ƙungiyar World Assembly of Muslim Youth [WAMY] da suka ba mu gudummawa wajen shirya wannan taron, “in ji Sheikh Ali”.

Taron shan ruwan dai ya sami halartar dukkanin shugabannin hukumar da mambobin ta da kuma ma’aikatanta tare da shugabannin kungiyar WAMY, da wasu manyan mutane da suka halarta.

Da yake nasa jawabin wakilin shugaban kungiyar Wamy Alhaji Sanusi, ya nuna jin daɗinsa da yadda wannan shan ruwa ya gudana, kuma ya tabbatar da cewar kungiyar su ƙungiya ce ta taimakon addinin musulunci da musulmi a ko ina suke, kuma kungiyar zata ci gaba da wannan aikin alherin da izinin Allah S.W.T.

Continue Reading

Addini

Ku taimakawa mabuƙata da Naman Sallah bisa halin matsin rayuwar da ake ciki – Limami

Published

on

Babban limamin masallacin juma’a na Alaramma Abubakar Ɗan Tsakuwa, da ke unguwar Ja’en Ring road Mallam Abdulkareem Aliyu, ya yi kira ga al’ummar Musulmi, da su kiyaye ƙa’idojin yanka Dabbobin Layyah, domin gujewa cin mushen Nama.

Mallam Abdulkareem Aliyu, ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u, lokacin da yake tsokacin huɗubar da ya gabatar ranar Sallar Idin da ya jagoranta a masallacin ranar Lahadi 17 ga watan Yunin 2024.

Ya ce a mafi yawan lokuta al’umma sukan yanka dabbobi amma rashin bin ƙa’idojin yanka yakan sanya wa su ci mushen nama ba tare da sun sani ba, a dan haka su tashi tsaye wajen sanin yadda ake yanka Dabbobin a mahanga ta addinin Musulunci.

A cewar sa, “Musulmai ku kwaɗaitu da yin sadakar naman layya musamman ma ga masu ƙaramin ƙarfi domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T, “in ji shi”.

Mallam Abdulkareem Aliyu, ya kuma ce, akwai buƙatar a kiyaye nau’ikan dabbobin da aka sahale ayi layya da su, waɗanda suka haɗar da nau’in Sa ko Saniya, da kuma Raƙumi ko Raƙuma (Taguwar), ko kuma Rago ko Tinkiya, ko Akuya ko kuma Ɗan Akuya.

Wannan dai na zuwa ne bayan da al’ummar Musulmin Duniya suka gudanar da babbar Sallah, a jiya Lahadi 16 ga watan Yunin shekarar 2024.

Continue Reading

Addini

An ga jinjirin watan Zul-Hijjah a Najeriya, ranar Lahadi 16 ga watan Yuni Babbar Sallah

Published

on

Fadar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Abubakar Sa’ad na uku, ta sanar da ganin jinjirin watan Zul-Hijjah na shekarar 1445.

Hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmin ta fitar, mai ɗauke da sa hannun Wazirin Sakkwato, kuma shugaban kwamitin duban wata Farfesa Sambo Wali Junaid.

Sanarwar ta kuma ce duba da ganin jaririn watan na Zul-Hijjah da akayi a jiya Alhamis, hakan ya tabbatar da cewar yau Juma’a ɗaya ga watan Zul-Hijjah, wanda za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan Yunin 2024.

Tun dai a jiya Alhamis hukumomi a ƙasar Saudiyya suka sanar da ganin Jaririn watan na Zul-Hijjah, lamarin da ya kasance za’ayi tsayuwar Arafa a ranar Asabar 15 ga watan Yunin 2024, yayin da za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan na Yuni.

Kafar Dala FM Kano, ta rawaito cewa, kawo yanzu dai maniyyata aikin hajjin bana da dama ne ke ci gaba da shiga ƙasa mai tsarki, a ƙoƙarin su na zuwa domin sauke Farali.

Continue Reading

Trending