Connect with us

Manyan Labarai

Akwai rashin adalci kan dakatar da Sanata Abdul Ningi, zamu bibiyi al’amarin – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta ƙasa da ƙasa ta International Human Rights Commission, ta soki lamirin majalisar dattawan ƙasar nan, kan dakatar da sanatan Bauchi ta Tsakiya Sanata Abdul Ahmed Ningi, har na tsawon watanni uku.

Daraktan ƙungiyar a ƙasar nan Kyaftin Abdullahi Bakoji Adamu mai ritaya, ne ya bayyana hakan a yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM Kano, a yammacin Asabar ɗin nan, ya ce akwai rashin adalci a fagen dakatar da Sanata Ningi, a dan haka ne ma suke kira da’a dawo da shi kan kujerar sa.

Idan dai ba’a manta ba tun a ranar Talata 12 ga watan Maris da muke ciki na shekarar 2024, ne majalisar dattawan ƙasar nan ta dakatar da Sanata Abdul Ahmed Ningi, daga ayyukan majalisar har zuwa watanni uku masu zuwa, biyo bayan zargin sa da zubar da kimar majalisar.

Sanata Abdul Ningi, dai ya zargi majalisar da yin cushe a kasafin kuɗin 2024, a hirar sa da sashen Hausa na BBC, lamarin da bai yiwa majalisa daɗi ba inda har ta kafa wani kwamiti, a ranar gabatar da sakamakon binciken kwamitin ne ma sanatocin suka kaɗa ƙuri’ar dakatar da Ningi.

Kyaftin Abdullahi Bakoji mai ritaya, ya kuma ce hedikwatar ƙungiyar su ta basu wa’adin kwanaki biyar da su bibiyi abinda majalisa suka yi akan dakatar da Sanata Ningi, daga bisani su rubuta su sanar da sakamakon binciken su ga hedikwatar ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ɗin.

“Mun fashimci cewar akwai rashin adalci kan dakatar da Ningi, saboda ya faɗi gaskiya wanda hakan ya nuna cewar ba wanda ya yi laifi ake hukunta wa ba, face wanda ya gano laifin wanda hakan babban kuskure ne da ba zai haifar wa da Najeriya Ɗa mai ido ba, “in ji Bakoji”.

Wakilin gidan rediyon Dala FM Kano ya rawaito cewa, Bakoji ya ci gaba da cewa, matuƙar irin hakan ya ɗore babu makawa Najeriya tana shirin wargajewa ke nan.

Manyan Labarai

Za’a ɗauki mataki akan duk wanda yake da hannu Gini ya ruftawa mutane a Kuntau – Ƙaramar hukumar Gwale.

Published

on

Yayin da wani ginin Bene mai hawa biyu ya danne aƙalla sama da Leburori goma a unguwar Kuntau kusa da KEDCO, a safiyar yau Juma’a, Shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Gwale Abubakar Mu’azu Mojo, ya ce za’a ɗauki mataki akan dukkan wanda aka samu da laifi har al’amarin ya faru.

Abubakar Mu’azu Mojo, ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da manema labarai, yayin da ya ziyarci gurin da lamarin ya faru lokacin da ake ci gaba da aikin ceto mutanen.

Mojo, ya kuma ce babu makawa za’a ɗauki matakin doka akan duk wanda aka samu da hannu akan faruwar lamarin, kama daga ɗan kwangilar da aka bai wa aikin ginin, zuwa kuma mamallakin gidan.

Rahotanni sun bayyana cewa zuwa tsakar ranar yau aƙalla mutane bakwa aka ciro daga ƙasan ginin shida daga cikin su basa iya motsa jikin su, yayin da hukumomi suka ci gaba da gudanar da aikin ceto sauran mutanen da ginin ya danne.

Continue Reading

Manyan Labarai

Sulhu da ƴan Bindiga ba zai haifar da Ɗa mai ido ba – Human Rights 

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta ƙasa da ƙasa wato International Human Rights Commission, ta ce sulhu da ƴan bindiga ba zai haifar da Ɗa mai ido ba a ƙasar nan.

Babban daraktan ƙungiyar Kyaftin Abdullahi Bakoji Adamu mai ritaya, shi ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM Kano.

Ya ce kasancewar ƴan bindigar basu da wata manufa bai kamata ayi sulhu da su ba, mai-makon hakan yafi dacewa a rinƙa ɗaukar tsauttsauran mataki akan su duba da yadda suke cutar da al’umma.

Ya kuma ce batun da mai bai wa shugaban ƙasa akan sha’anin tsaro Malam Nuhu Ribaɗo, ya yi a baya baya nan, kam cewar an fara samun fashimtar juna da wasu daga cikin ƴan Bindigar da suka addabi mutane a sassan ƙasar nan, a wani ɓangare ma kama da yin sulhu da su, ya faɗi hakan ne kawai amma hakan ba zai haifar da Ɗa mai ido ba.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gwamnatin Kano ta kulle wata makaranta mai zaman kan ta a jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta rufe wata makaranta mai suna Golden Crown International School a jihar, da ke yankin Sabon gari, bisa zargin an fake da sunan makarantar ana haɗa magani mara inganci mai-makon koyar da karatu a ciki.

Shugaban kwamitin yaki da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya na jihar Kano General Gambo Mai Aduwa Mai ritaya, ne ya bayyana hakan, a lokacin da Kwamitin ya kai wani sumame da karfe uku da rabi na daren jiya Talata.

Rahotanni sun bayyana cewa makarantar tana kan titin Zungero da ke cikin ƙaramar hukumar Fagge a jihar Kano, wanda bayan samun bayanan sirri aka ɗauki matakin kulle ta.

Mai Aduwa, ya ƙara da cewar tsarin gurin ta waje ya nuna makaranta ce amma kuma sai ake sarrafa magani da ake zargin ingancin sa da bai kai yadda ya kamata ba, tare da ajiye Allurai da kayan haɗa magani cikin ajujuwan mai-makon ɗalibai.

“Za mu faɗaɗa bincike akan al’amarin dan sanin matakin da za mu ɗauka na gaba, “in ji shi”.

Suma masu gadin gurin da muka zanta da su sun bayana cewar, aikin gadi kawai suke yi amma basu da masaniyar abubuwan dake gudana a cikin makarantar, da ake zargin ana sarrafa magani mara ingani da ajiye shi a muhalin da ake zargin bai yi dai-dai da tsarin doka ba.

Wakilinmu Abba Isah Muhammad ya rawaito cewa shugaban kwamitin ya ce, zai ci gaba da bibiyar guraren dake yin abubuwan da za su kawo koma baya ga harkokin lafiya, da ci gaban jihar Kano, musmman wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya.

Continue Reading

Trending