Manyan Labarai
Akwai rashin adalci kan dakatar da Sanata Abdul Ningi, zamu bibiyi al’amarin – Human Rights
Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta ƙasa da ƙasa ta International Human Rights Commission, ta soki lamirin majalisar dattawan ƙasar nan, kan dakatar da sanatan Bauchi ta Tsakiya Sanata Abdul Ahmed Ningi, har na tsawon watanni uku.
Daraktan ƙungiyar a ƙasar nan Kyaftin Abdullahi Bakoji Adamu mai ritaya, ne ya bayyana hakan a yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM Kano, a yammacin Asabar ɗin nan, ya ce akwai rashin adalci a fagen dakatar da Sanata Ningi, a dan haka ne ma suke kira da’a dawo da shi kan kujerar sa.
Idan dai ba’a manta ba tun a ranar Talata 12 ga watan Maris da muke ciki na shekarar 2024, ne majalisar dattawan ƙasar nan ta dakatar da Sanata Abdul Ahmed Ningi, daga ayyukan majalisar har zuwa watanni uku masu zuwa, biyo bayan zargin sa da zubar da kimar majalisar.
Sanata Abdul Ningi, dai ya zargi majalisar da yin cushe a kasafin kuɗin 2024, a hirar sa da sashen Hausa na BBC, lamarin da bai yiwa majalisa daɗi ba inda har ta kafa wani kwamiti, a ranar gabatar da sakamakon binciken kwamitin ne ma sanatocin suka kaɗa ƙuri’ar dakatar da Ningi.
Kyaftin Abdullahi Bakoji mai ritaya, ya kuma ce hedikwatar ƙungiyar su ta basu wa’adin kwanaki biyar da su bibiyi abinda majalisa suka yi akan dakatar da Sanata Ningi, daga bisani su rubuta su sanar da sakamakon binciken su ga hedikwatar ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ɗin.
“Mun fashimci cewar akwai rashin adalci kan dakatar da Ningi, saboda ya faɗi gaskiya wanda hakan ya nuna cewar ba wanda ya yi laifi ake hukunta wa ba, face wanda ya gano laifin wanda hakan babban kuskure ne da ba zai haifar wa da Najeriya Ɗa mai ido ba, “in ji Bakoji”.
Wakilin gidan rediyon Dala FM Kano ya rawaito cewa, Bakoji ya ci gaba da cewa, matuƙar irin hakan ya ɗore babu makawa Najeriya tana shirin wargajewa ke nan.
Manyan Labarai
Gundura da ake zargi da sarewa Ɗan Bijilante hannu da fasa motar ƴan sanda ya shiga hannu
Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta samu nasarar cafke wani Matashi mai suna Inuwa Zakari ɗan shekara 24, wanda akafi sani da Gundura, wanda ake zargi da sarewa wani Ɗan Bijilante hannu, da kuma fasa motar Ƴan Sanda, da wasu Laifuka
Kakakin rundunar ƴan sandan SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar da ya aikowa Dala FM a daren Litinin, Kiyawa ya ce Matashi Gundura sun daɗe suna neman sa ruwa a jallo bisa zargin sa da tarin Laifuka.
“Gundura ya kasance abokin fitaccen ɗan Dabar nan Abba Burakita ɗa unguwar Ɗorayi da ya rasu a baya, kuma har kotu ma muka gurfanar da shi daga baya ya fita amma bai dai na abinda ya ke yi ba, a ranar zaɓen ƙananan hukumomin Kano, da ya shigo yana yunƙurin tayar da hankalin al’umma jami’an mu suka kama shi, “in ji SP Kiyawa”.
Har ila yau, Abdullahi ya ce an kama Gundura da wukake guda biyu a wani waje na matattarar Yan Daba da suke kira “Jungle” a Unguwar Dorayi.
Rundunar ƴan sandan ta ce ta kuma cafke ƙarin wasu matasa 14, da ake zargin su da aikata maban-banta laifuka, inda aka kama su a tsakanin 25 ga zuwa 27 na watan Oktoban 2024.
SP Kiyawa ya ƙara da cewa yanzu haka waɗanda ake zargin ana ci gaba da bincike a kan su a babban sashin binciken manyan laifuka na CID, da ke hedikwatar rundunar da ke Bompai a Kano, kuma da zarar an kammala za’a gurfanar da su a gaban kotu.
Manyan Labarai
Ku zauna lafiya yayin zaɓen ƙananan hukumomin da ake gudanarwa a Kano – Kwankwaso
Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi kira ga al’umma da su tabbatar da an samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a zaɓen ƙananan hukumomin da ake gudanarwa yau a Kano.
Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kaɗa ƙuri’a a mazaɓar sa ta Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a Kano.
Ya kuma ce akwai buƙatar al’ummar jihar su fita rumfunan zaɓen su kaɗa ƙuri’un su domin ƙara inganta Demukuraɗiyya a jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.
Kwankwaso ya kuma jaddada wa al’ummar jihar cewar gwamnatin Kano za ta ci gaba da ayyukan alheri a faɗin jihar, domin samar da ci gaban Jama’a.
A ranar Asabar ɗin nan ne dai ake gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar Kano 44, wanda shugabannin fa za’a zaɓa za su shafe tsawon shekaru uku-uku a karagar mulki.
Kafin wannan rana an dai samu cece-kuce akan batun zaɓen, wanda a ranar Talatar da ta gabata wata babbar kotun tarayya da ke jihar Kano, ta dakatar da shugabancin hukumar zaɓen ta jihar Kanseic, da umartar Ƴan sandan jihar su ƙairacewa shiga aikin zaɓen.
Ko da dai a jiya Juma’a babbar kotun jahar Kano ƙarƙashin mai Shari’a Sunusi Ado Ma’aji, ta umarci hukumar zaɓen ta gudanar da zaɓen a yau Asabar, tare da umartar Ƴan sandan su shiga aikin zaɓen, ko da dai wasu mazauna jihar sun shaidawa Dala FM cewar, ba su ga jami’an ƴan sanda ba a wuraren zaɓen.
Jami’an tsaron da aka gani sun haɗar da ƴan Karota, da na Hisbah, da kuma ƴan Bijilante, da jami’an rundunar tsaro da ke yaƙi da ƙwacen Waya da faɗan Daba da magance Shaye-shaye ta Anty Snaching Phone da ke Kano.
Manyan Labarai
Har yanzu jam’iyyu 6 ne suka cika ƙa’idar zaɓen ƙananan hukumomin da za a gudanar kuma babu APC a ciki – KANSEIC
Hukumar zaɓe ta jihar Kano (KANSIEC), ta bayyana sunayen jam’iyyu 6 a matsayin waɗanda suka cika ƙa’idar shiga zaben ƙananan hukumomin da za a gudanar ranar Asabar a Kano.
Shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Malumfashi ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan babbar kotun jaha ta tabbatar da halaccin hukumar zaben.
Farfesa Malumfashi ya bayyana cewar jam’iyyun da suka cika ƙa’idar sun haɗar da Jam’iyyar AA, AAC, Accord, ADC, da APM da kuma jam’iyyar NNPP mai mulki a jihar Kano.
Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, shugaban hukumar zaben ya bukaci hukumomin tsaro da su fito su kare rayuka da dukiyoyin al’umma a lokacin gudanar da zaben, kamar yadda babbar kotun jaha ta umarce su a hukuncin da ta yi da ranar Juma’a 25 ga watan Oktoban 2024.
A ranar Alhamis dai an jiyo yadda kwamoshina mai kula da harkokin yaɗa labarai da al’amuran Shari’a na hukumar zaɓe ta jihar Kano Kanseic, Lawan Badamasi, ya ce za su yi amfani da jami’an tsaron cikin gida domin samar da tsaro yayin zaɓen.
Ya ci gaba da cewa daga cikin jami’an tsaron cikin gidan akwai irin su ƴan Karota, da na Hisbah, da kuma Ƴan Bijilante, domin samar da tsaro idan ƴan sanda suka ƙauracewa shiga aikin zaɓen kamar yadda suka samu umarnin hakan daga wata babbar kotun tarayya da ke jihar Kano.
-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su