Connect with us

Manyan Labarai

Muna samun hadin kai dari bisa dari daga majalisar dokokin jihar kano:Engr Abba Kabir Yusif.

Published

on

Gwamnatin jihar kano ta ce tana samun hadin kai dari bisa dari daga majalisar dokokin jihar kano.

Gwamnan Kano Engr Abba Kabir Yusif ne ya bayyana hakan yayin taron walimar buda da ya jagoranta a daren Litinin din nan tare da yan majalisun dokokin jihar kano, da kuma yan majalisun dake wakiltar jihar kano a zauren majalisar dokoki ta kasa.

Engr Abba Kabir Yusif ya ce yana fatan wannan hadin kan da yake samu zai dore domin cigaba da hidimtawa al’ummar jihar kano kamar yadda sukayi alkawari yayin yakin neman zabe na shakarar 2023 da ta gabata.

Gwamnan ya kara da cewa sakamakon aikace – aikacen da al’ummar kudancin kasar nan ke samu ta bangaren babban dan kasuwar nan dan asalin jihar kano Alhaji Aliko Dangote, hakan tasa gwamnatin ta hada guiwa dashi domin itama kano ta amfana da irin wa’yannan ayyukan, inda yace nan bada jimawa za’ayi manyan titina guda biyu a jihar kano karkashin kulawar Aliko Dangote.

Daga bisani yayi kira ga ‘yan majalisun tarayya dasu kara kaimi wajen samowa jihar kano manyan ayyukan cigaba, kamar yadda wakilinmu na fadar Gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito mana.

Manyan Labarai

Jarabawar JAMB: An dakatar da duban tsaftar muhalli na watan Afrilun 2025 – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da aikin duban tsaftar muhalli na watan Afrilun 2025, domin bai wa ɗaliban da za su rubuta jarrabawar shiga manyan makarantun kasar nan JAMB, damar isa cibiyoyin zana jarrabawar a kan lokaci.

Kwamishinan muhalli da kula da sauyin yanayi na jihar Kano Dakta Dahir Hashim Muhammad ne ya sanar da hakan, a cikin wata sanarwa da daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar Sama’ila Garba Gwammaja ya fitar a ranar Alhamis.

Sanarwar ta ce, an dauki wannan matakin ne bayan nazari da tuntubar masu ruwa da tsaki, a kokarin bai wa daliban jihar Kano damar rubuta jarabawarsu ta JAMB, ba tare da wata matsala ba.

“Muna mai tabbatar wa mazauna Kano cewa, dakatarwar duban tsaftar muhallin na wucin gadi ne a iya wannan watan kawai, kuma za a ci gaba da aikin tsaftar muhallin a watan Mayun 2025, “in ji Dr. Ɗahir”

Kwamishinan ya kuma yi kira ga mazauna jihar Kano, da su ba hukuma hadin kai da fahimtar dalilin da ya sa aka yanke wannan hukunci, musamman na ganin cewa ayyukan tsaftar muhalli ba su ci karo da wasu muhimman abubuwan da ke faruwa a jihar ba.



Continue Reading

Manyan Labarai

Babu ɗaga Ƙafa tsakanin mu da Ƴan Daba da masu ƙwacen Waya a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Wayoyin jama’a da kuma daƙile Shaye-shayen kayan maye ta Anty Snaching Phone, ta gargaɗi matasan da suke addabar al’umma da faɗan Daba a cikin birnin jihar Kano, da su ƙauracewa hakan domin ba za su saurarawa dukkanin wanda ya faɗa komar su ba.

Kwamandan rundunar tsaron a jihar Kano Inuwa Salisu Sharaɗa, shi ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, ya ce duk wanda suka kama da laifi musamman ma na faɗan Daba, ko ƙwacen waya ko kuma sha da dillancin kayan maye, za a ɗauki tsattsauran mataki akan sa.

 

“Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu ƙwacen Wayoyin jama’a, da Faɗan Daba, da kuma masu Sha da dallancin kayan Maye a jihar Kano, kuma duk wanda mu ka kama sai mun miƙa shi gurin da ya dace don ɗaukar Mataki, “in ji Inuwa Sharaɗa”.

 

Ya kuma buƙaci iyaye da su ƙara sanya idanu wajen kula akan shige da ficen ƴaƴan su, ta yadda za su zama ababen koyi a tsakanin al’umma.



Continue Reading

Manyan Labarai

Za’a hukunta duk ma’aikacin Shari’ar da aka samu da laifi – Babbar Jojin Kano

Published

on

Babbar jojin Kano mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jaddada cewar kwamitin ladabtarwa na hukumar Shari’a a jihar, zai hukunta duk wani ma’aikaci a tsagin Shari’a matuƙar aka same shi da laifin cin-hanci da rashawa.

Mai Shari’a Dije Aboki ta bayyana hakan ne a yayin taron ƙarawa juna sani wanda hukumar shari’ar ta gudanar ranar Talata, a ɗakin taro na Murtala Muhammad Library da ke Kano.

Taron an shirya shi ne don tunasar da sabbin ma’aikatan Shari’a, akan nauyin da ya hau kan su don mayar da hankali sosai akan batun gujewa cin-hanci da rashawa.

Babbar mai Shari’ar Dije Abdu Aboki, ta bayyana cewar akwai takaddu masu ɗauke da lambobin wayarta da aka liƙe a bangon kotuna, kuma duk wanda aka yi wa ba dai-dai ba zai iya sanar da ita ta kan lambobin kuma za a dauki mataki akan duk ma’aikacin da aka samu da laifi.

Wakilin tashar Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, a yayin taron taron ma’aikatan Shari’a da al’umma da dama ne suka samu damar halarta.



Continue Reading

Trending