Connect with us

Manyan Labarai

Gwamnan Kano ya kafa kwamiti guda biyu da zai binciki tsohuwar gwamnatin Ganduje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da wani kwamati guda biyu da za su bincike akan yadda tsohuwar gwamnatin Dr Abdullahi Umar Ganduje ta gudanar da tafiyar da gwamnatin ta a shekaru takwas da suka gabata.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ne ya jagoranci ƙaddamar da kwamititocin, wanda kwamitin na farko zai yi bincike akan yadda akayi tasarrafi da kadarorin gwamnati na ciki da wajen jihar kano, wanda suke zargin an sayar ko mallakawa kai da kuma mallaka wa ‘ya’ya ba bisa ka’ida ba.

Kwamati na biyu kuma da zai yi bincike akan yadda aka gudanar da rikice rikicen zabe, da yadda akayi amfani da matasa wajen tayar da hankali da salwantar da rayukan al’ummar da ba suji ba kuma basu gani ba.

A cewar gwamnan, “A bisa zargin da muke yiwa tsohuwar gwamnatin ta Ganduje, ne ya sa muka naɗa ingantattun mutane, da za su kwashe tsawon watanni uku suna gudanar da wannan bincike, “in ji Gwamna Abba Kabir”.

Ya kuma ƙara da cewa wannan bincike ba sunayin sa ba ne domin muzgunawa wani ko wata, ya ce alkawarin da suka yiwa al’ummar jihar kano, da kuma rantsuwa da su kayi da Al-kur’ani, ne ya sa zasu gudanar da wannan bincike.

Abba Kabir, yana mai cewa duk wanda aka kama da laifi za’a hukunta shi kamar yadda doka ta tanadar.

Wakilinmu na fadar gidan gwamnatin Kano Abba Haruna Idris, ya rawaito wamnan ya kuma ja hankalin kwamitin da suyi bincike mai karfi a bangaren yadda aka gudanar da yanke – yanken gonaki da burtalai, da makarantu da makabartu domin mayarwa da al’ummar jihar kano hakkinsu, ya kuma ja hankalin Kwamatin da suyi aiki tsakani da Allah yayin gudanar da binciken.

Manyan Labarai

Zamu ƙone duk kayayyaki marasa inganci da muka kama da zarar an gama shari’u – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta ƙone dukkanin kayayyaki marasa inganci da ta kama, da zarar an kammala dukkanin shari’un da suke a gaban Kotu.

Kwamishinan ma’aikatar ciniki da masana’antu, Adamu Aliyu Kibiya, ne ya tabbatar da hakan, a yayin wata ziyara ta musamman da ya kai hukumar kula da ingancin kayayyaki ta jihar Kano, a yammacin yau Alhamis.

Amadadin Kwamishinan babban sakataren ma’aikatar, Muhammad Yusuf Ɗan-duwa, ya ce, da zarar an kammala Shari’un da masu kayan za’a ƙone su baki ɗaya.

“A bisa al’adar ma’aikatar ciniki da masana’antu, dama duk sabon Kwamishina idan ya zo yana ziyarartar hukumomin da suke da jiɓi da ma’aikatar domin duba irin aikace-aikacen su da sauran abinda ba’a rasa ba, hakan ya sa ma Kwamishinan ya ziyarci hukumar a yau, “in ji Ɗan-duwa”.

 

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, babban sakataren ya ƙara da cewa, ziyarar da Kwamishinan ciniki da masana’antun Alhaji Adamu Aliyu Kibiya, ya kai hukumar kula da ingancin kayayyakin, itace ta farko.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta ci gaban mai haƙan rijiya ne – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights, ta ce ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta, ci gaban mai haƙan rijiya ne, domin ba zai magancewa ma’aikatan matsalolin su ba.

Daraktan ƙungiyar reshen jihar Kano Alhaji Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da wakilinmu na ƴan Zazu Hassan Mamuda Ya’u, a yau Laraba, lokacin da yake tsokaci a kan bikin ranar ma’aikata da ake gudanarwa yau a Najeriya.

Ya kuma ce kasancewar ƙarin albashin ba zai ragewa ma’aikatan wata damuwa ba, sai dai ma ya tunzura ma’aikatan, bai kamata ƙungyoyin ƙwadago su amine da tsirarun ƙarin ba.

“Matukar gwamnatin tarayya za ta rinƙa tunzura ma’aikata da irin wannan tsirarun albashin babu makawa zamu gurfanar da ita a gaban kotu, “in ji Galadanci”.

Umar Sani ya kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta lalubo sabbin hanyoyi da za’a ƙarawa ma’aikatan albashi mai tsoka wanda zai rinƙa magance musu wasu matsalolin su na yau da kullum.

Har ila yau, suma ƙungiyoyin ƙwadago a ƙasar nan, sun yi fatali da ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta da kashi 25 cikin ɗari, da kuma kashi 35 a cikin ɗari.

Ƙungiyoyin ƙwadago da dama na NLC, da TUC, da sauran ƙungiyoyi ne suka gudanar da taron ranar ma’aikan a sassan jahohin ƙasar nan.

Continue Reading

Manyan Labarai

Kayan aikin ginin da ya ruftawa magina a Kuntau ba masu inganci ba ne – Cibiyar masu Taswirar Zane-zanen Muhalli

Published

on

Cibiyar masu tasawirar zane-zanen muhalli ta ƙasa reshen jihar kano, tayi Allah wa dai da kayan da akayi wani ginin Bene da shi mai hawa uku, da ya faɗo akan wasu magina a cikin unguwar Kuntau da ke yankin karamar hukumar Gwale a jihar kano.

Mataimakin shugaban ƙungiyar na kasa Arct Ali Mukhtar, ne ya bayyana hakan a lokacin da cibiyar takai ziyara wajen da al’amarin ya faru.

Ya ce dukkanin kayan da aka yi aikin ginin benen da su ba masu inganci ba ne.

A nasa jawabin shugaban cibiyar a nan nano Arct Bashir Hassan Hanga, kira ya yi ga gwamnatin jihar kano, da ta hana duk masu irin wannan gine-gine ba tare da sahalewar hukumar tsara birane ba wato Knupda, ta kuma ɗauki mataki akan mamallakin wannan gini da ya rushe a kan maginan.

Wakilin mu Shamsu Dau Abdullahi ya rawaito cewa dukkanin tawagar cibiyar tsara gine-ginen, sun ce za su ziyarci asibitin Murtala Muhammad, domin duba mutanen da gini ya fadowa da kuma zuwa ta’aziya gidan waɗanda suka rasu su uku.

Continue Reading

Trending