Connect with us

Manyan Labarai

Doka za ta yi aiki akan duk masu tayar da hankalin al’umma yayin bikin Sallah – Ƴan Sandan Kano.

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce ba za ta saurarawa ɓata garin da suka ce ba za’a zauna lafiya ba, a yayin bikin ƙaramar Sallah.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan a zantawar sa da wakiliyar mu A’isha Shehu Kabara, ya ce duk wasu gungun mutane da suka ce zasu ɗaukko muggan makamai da zummar tayar da hankalin al’umma ko kuma illata mutane lashakka doka za tayi aiki a kan su.

“Duk wanda ya ce ba za’a zauna lafiya ba a yayin bikin ƙaramar Sallar mu kan mu ba zamu bar shi ya nutsu ba, za muyi duk abinda ya kamata na ganin cewa an kare irin waɗannan abubuwa, “in ji SP Kiyawa”.

Ya ƙara da cewa yanzu haka Kwamishinan ƴan sandan Kano CP Muhammad Usaini Gumel, ya riga ya bada umarnin baza jami’an tsaron ƴan sandan su, kuma ciki har da na farin kaya da kuma wadata su da kayan aiki, domin yin dukkan abinda ya kamata wajen ganin an tsare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

Rundunar ƴan sandan Kano, ta kuma shawarci masu ababen hawa da su kula yayin tuƙi a kan hanya da cikin unguwanni a yayin bikin ƙaramar Sallah, tare da kaucewa gudun ganganci, domin kaucewa afkuwar haɗura.

“Iyaye ku kula da ƴaƴan ku a yayin bikin sallar domin gujewa ɓatan su ko kuma faɗawa komar ɓata gari, a cewar sa”.

Wannan dai na zuwa ne yayin da ake sa ran gudanar da bikin ƙaramar Sallah, a ranar Laraba 10 ga watan Afrilu na shekarar 2024.

Manyan Labarai

Kayan aikin ginin da ya ruftawa magina a Kuntau ba masu inganci ba ne – Cibiyar masu Taswirar Zane-zanen Muhalli

Published

on

Cibiyar masu tasawirar zane-zanen muhalli ta ƙasa reshen jihar kano, tayi Allah wa dai da kayan da akayi wani ginin Bene da shi mai hawa uku, da ya faɗo akan wasu magina a cikin unguwar Kuntau da ke yankin karamar hukumar Gwale a jihar kano.

Mataimakin shugaban ƙungiyar na kasa Arct Ali Mukhtar, ne ya bayyana hakan a lokacin da cibiyar takai ziyara wajen da al’amarin ya faru.

Ya ce dukkanin kayan da aka yi aikin ginin benen da su ba masu inganci ba ne.

A nasa jawabin shugaban cibiyar a nan nano Arct Bashir Hassan Hanga, kira ya yi ga gwamnatin jihar kano, da ta hana duk masu irin wannan gine-gine ba tare da sahalewar hukumar tsara birane ba wato Knupda, ta kuma ɗauki mataki akan mamallakin wannan gini da ya rushe a kan maginan.

Wakilin mu Shamsu Dau Abdullahi ya rawaito cewa dukkanin tawagar cibiyar tsara gine-ginen, sun ce za su ziyarci asibitin Murtala Muhammad, domin duba mutanen da gini ya fadowa da kuma zuwa ta’aziya gidan waɗanda suka rasu su uku.

Continue Reading

Manyan Labarai

Majalisa ta amince da dokar gwajin cutar Ƙanjamau da ta Sikila kafin aure a Kano

Published

on

Majalisar Dokokin jahar kano ta amince da dokar yin gwajin cutar kanjamau da ta Sikila da kuma sauran cututtuka kafin yin aure.

Da yake Jawabi akan kafa dokar, Shugaban Majalisar dokokin jahar kano Alhaji Jibril Isma’il Falgore, ya ce dokar za ta daƙile yaɗuwar cututtuka a tsakanin ma’aurata da yaɗa su ga iyali da ma al’umma baki ɗaya.

Har ila yau, dokar ta ba da damar yin gwajin cututtuka masu haɗari da wuyar magani kafin yin aure, tare da tanadin hukunci mai tsanani ga duk wanda yaƙi yin biyayya ga dokar.

Mataimakin Akawun Majalisar kuma babban Sakatare Alhaji Nasiru Magaji, ne ya gabatar da karatu na uku akan dokar kafin amincewa da ita a ranar Litinin.

Continue Reading

Manyan Labarai

Za’a ɗauki mataki akan duk wanda yake da hannu Gini ya ruftawa mutane a Kuntau – Ƙaramar hukumar Gwale.

Published

on

Yayin da wani ginin Bene mai hawa biyu ya danne aƙalla sama da Leburori goma a unguwar Kuntau kusa da KEDCO, a safiyar yau Juma’a, Shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Gwale Abubakar Mu’azu Mojo, ya ce za’a ɗauki mataki akan dukkan wanda aka samu da laifi har al’amarin ya faru.

Abubakar Mu’azu Mojo, ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da manema labarai, yayin da ya ziyarci gurin da lamarin ya faru lokacin da ake ci gaba da aikin ceto mutanen.

Mojo, ya kuma ce babu makawa za’a ɗauki matakin doka akan duk wanda aka samu da hannu akan faruwar lamarin, kama daga ɗan kwangilar da aka bai wa aikin ginin, zuwa kuma mamallakin gidan.

Rahotanni sun bayyana cewa zuwa tsakar ranar yau aƙalla mutane bakwa aka ciro daga ƙasan ginin shida daga cikin su basa iya motsa jikin su, yayin da hukumomi suka ci gaba da gudanar da aikin ceto sauran mutanen da ginin ya danne.

Continue Reading

Trending