Connect with us

Siyasa

Gwamnan Kano ya sake naɗa Ogan ɓoye muƙami da wasu mutane takwas

Published

on

A ƙoƙarin sa na ci gaba da kawo cigaba a jihar sa Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sake naɗa Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, a matsayin mai bashi shawara a kan harkokin matasa da wasanni, tare da naɗa wasu mutane takwas waɗanda za su taimaka masa a fannoni daban-daban.

Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Litinin, ya ce Gwamnan ya amince da naɗa mutanen ne kamar haka;

An naɗa Farfesa Ibrahim Magaji Barde, a matsayin mai bai wa gwamnan shawara na musamman a kan harkokin tattara kuɗaɗen shiga (IGR).

Sai kuma Dr. Abdulhamid Danladi, da aka naɗa shi a matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman kan harkokin kasashen waje na II.

An kuma naɗa Engr. Bello Muhammad Kiru, mai bashi shawara na musamman kan albarkatun ruwa.

Yayin da aka sake naɗa Ambasada Yusuf Shuaibu Imam (Ogan Boye) a matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman a kan harkokin matasa da wasanni a jihar.

Har ila yau, Dr. Nura Jafar Shanono, shi kuma an ɗauke shi daga mai ba da shawara na musamman kan albarkatun ruwa zuwa Manajan Darakta, a ma’aikatar Ruwa da Gine-gine (WRECA) ta jihar Kano.

Shi kuwa Baba Abubakar Umar, ya samu sauyi daga mai bai wa gwamna Kano shawara na musamman ga harkokin makarantu masu zaman kansu, zuwa ma’aikatar dake kula da ma’aikatan wucin gadi.

An kuma nada Hon. Nasir Mansur Muhammad, a matsayin shugaban hukumar , ƙanana da Matsakaitan Masana’antu (SMEs).

Yayin da Aminu Hamidu Bako Kofar Na’isa ya zama mataimakin shugaban Hukumar kula da Albarkatun Noma da Raya Karkara ta Kano (KNARDA).

Shi kuwa Engr. Mukhtar Yusuf, an naɗa shi a matsayin mataimakin shugaban hukumar kula Albakatun ruwa Ruwa da Gine Gine (WRECA).

Sanusi Bature ya kuma ce, naɗin ya fara aiki ne nan take, inda Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kuma taya su murna tare da fatan alkhairi.

Hangen Dala

Lauyoyin gwamnatin Kano sun bukaci a kamo Ganduje

Published

on

Babbar kotun jaha mai lamba 7 karkashin jagorancin mai sharia Amina Adamu ta sanya karfe biyu da rabi na ranar yau dan bayyana matsayarta akan batun gurfanar da tsohon gwamnan kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa da wasu mutane.

A zaman kotun na yau lauyoyin gwamnatin jaha sun bayyana wa kotun cewa an sadar da sammace ga wadanda ake kara ta hanyar kafafen yada labarai kamar yadda kotun ta yi umarni tun a baya amma wadanda ake kara basu samu damar halartar kotun ba dan haka ya roki ko dai a kamo su ko kuma kotun ta ci gaba duk da cewar basa gaban kotun.

Sai dai lauyan wanda ake kara na 6 barrister Nuraini Jimo SAN ya yi suka inda ya bayyana cewar kotun ta dakata tun da sun daukaka kara ya kuma bayyana cewar kotun bata da hurumi sannan kunshin tuhume-tuhumen yana dauke ta kura-kurai.

Kotun zata bayyana matsayarta a yau da rana.

Tun da farko gwamnatin kano ta yi karar Ganduje da mutane 6 bisa zargin almundahana akan kudi sama da Naira Biliyan 4 da aka yi zargin sun sayarda wasu filaye sun raba kudin.

Continue Reading

Labarai

Da Dumi Dumi:- EL Rufai ya kai karar majalisar dokoki

Published

on

Tsohon Gwamna jahar Kaduna Mal. Nasir elrufai ya Maka majalisar Dokokin jahar Kaduna a gaban Kotu a bisa bata Masa Suna da majalisar tayi na cewa Gwamnatin sa ta sace kudaden jahar da Suka naura naira miliyan dubu Dari Hudu.

Tsohon Gwamna ya shigar da karar ce, a Gaban babbar kotun taraiyya dake NDA Kaduna a safiyar Laraban nan 26 ga watan Yuni 2024.

Inda ya bukaci Kotun data tursasa majalisar ta bashi hakuri a bainar jama’a, sakamakon Kazafin da Yan majalisan Suka yi masa da mukarraban Gwamnatinsa data gabata.

 

Karin bayani na nan tafe….

Continue Reading

Siyasa

Zauren jam’iyyun haɗin kan kasa IPAC sun cire shugaban jam’iyyar LP na Kano Abdullahi Raji daga cikin tafiyar su 

Published

on

Sakataren zauren jam’iyyun haɗin kan kasar nan, IPAC na ƙasa reshen jihar Kano, kuma shugaban jam’iyyar APM na Kano Honarable Nuhu Idris, ya ce sun cire shugaban jam’iyyar LP na jihar Kano Abdullahi Raji daga cikin tafiyar su ta IPAC, baki ɗaya.

Sakataren na IPAC, Nuhu Idris ya ce sun dauki wannan mataki ne bisa yadda Rajin ke amfani da kungiyar CUPP, da rusassun jam’iyyun kasar nan suka samar a baya, a dan haka, duk wata jam’iyyar dake da rijista a yanzu na ƙarƙashin IPAC.

Ya kuma ce dokar da ta kafa IPAC, ba ta bai wa ɗan kowacce jam’iyya damar shiga hurumin wata jam’iyyar ba kamar yadda Rajin ke ƙoƙarin yi a rikicin dake faruwa a jam’iyyar APC a nan jihar Kano.

Shugaban jam’iyyar APM, ɗin Honarable Nuhu Idris, ya ce sun cire Rajin daga tafiyar ta IPAC ne, sakamakon wata sanarwa da ya fitar, ya ce, ka da hukumar zaɓe INEC, ta yi watsi da shugaban mazaɓar Ganduje, wanda hakan ba dai-dai ba ne a dokance, dan haka, suka fitar da shi daga cikin tafiyar tare da sanar da shugabancin jam’iyyar sa na kasa.

Continue Reading

Trending