Siyasa
Gwamnan Kano ya sake naɗa Ogan ɓoye muƙami da wasu mutane takwas

A ƙoƙarin sa na ci gaba da kawo cigaba a jihar sa Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sake naɗa Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, a matsayin mai bashi shawara a kan harkokin matasa da wasanni, tare da naɗa wasu mutane takwas waɗanda za su taimaka masa a fannoni daban-daban.
Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Litinin, ya ce Gwamnan ya amince da naɗa mutanen ne kamar haka;
An naɗa Farfesa Ibrahim Magaji Barde, a matsayin mai bai wa gwamnan shawara na musamman a kan harkokin tattara kuɗaɗen shiga (IGR).
Sai kuma Dr. Abdulhamid Danladi, da aka naɗa shi a matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman kan harkokin kasashen waje na II.
An kuma naɗa Engr. Bello Muhammad Kiru, mai bashi shawara na musamman kan albarkatun ruwa.
Yayin da aka sake naɗa Ambasada Yusuf Shuaibu Imam (Ogan Boye) a matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman a kan harkokin matasa da wasanni a jihar.
Har ila yau, Dr. Nura Jafar Shanono, shi kuma an ɗauke shi daga mai ba da shawara na musamman kan albarkatun ruwa zuwa Manajan Darakta, a ma’aikatar Ruwa da Gine-gine (WRECA) ta jihar Kano.
Shi kuwa Baba Abubakar Umar, ya samu sauyi daga mai bai wa gwamna Kano shawara na musamman ga harkokin makarantu masu zaman kansu, zuwa ma’aikatar dake kula da ma’aikatan wucin gadi.
An kuma nada Hon. Nasir Mansur Muhammad, a matsayin shugaban hukumar , ƙanana da Matsakaitan Masana’antu (SMEs).
Yayin da Aminu Hamidu Bako Kofar Na’isa ya zama mataimakin shugaban Hukumar kula da Albarkatun Noma da Raya Karkara ta Kano (KNARDA).
Shi kuwa Engr. Mukhtar Yusuf, an naɗa shi a matsayin mataimakin shugaban hukumar kula Albakatun ruwa Ruwa da Gine Gine (WRECA).
Sanusi Bature ya kuma ce, naɗin ya fara aiki ne nan take, inda Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kuma taya su murna tare da fatan alkhairi.

Baba Suda
Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.
Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.
Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Labarai
Tsohon shugaban majalisar Dattawa Ahmad Lawan ya ƙaryata ficewar sa daga APC zuwa SDP

Tsohon shugaban majalisar Dattawa Ahmad Lawan, ya musanta wata jita-jita da ake yaɗawa kan cewar ya fice daga cikin jam’iyyar APC mai mulki a ƙasa, zuwa SDP, al’amarin da ya ce bashi da tushe ballantana makama.
A cikin wata sanarwar da mashawarci na musamman ga tsohon Sanatan a kafafen yaɗa labarai Ezrel Tabiowo, ya fitar a jiya Lahadi, ta ce jita-jitar da ake yaɗawa na cewar Ahmad Lawan ya fice daga jam’iyyar ta APC, ƙarya ce tsagwaronta.
Jaridar Daily trust ta ruwaito cewar, sanarwar ta kuma ce, har yanzu Ahmad Lawan ɗan Jam’iyyar APC ne, kuma yana biyayya ga jam’iyyar, wadda yake alfahari da ita.

Hangen Dala
Lauyoyin gwamnatin Kano sun bukaci a kamo Ganduje

Babbar kotun jaha mai lamba 7 karkashin jagorancin mai sharia Amina Adamu ta sanya karfe biyu da rabi na ranar yau dan bayyana matsayarta akan batun gurfanar da tsohon gwamnan kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa da wasu mutane.
A zaman kotun na yau lauyoyin gwamnatin jaha sun bayyana wa kotun cewa an sadar da sammace ga wadanda ake kara ta hanyar kafafen yada labarai kamar yadda kotun ta yi umarni tun a baya amma wadanda ake kara basu samu damar halartar kotun ba dan haka ya roki ko dai a kamo su ko kuma kotun ta ci gaba duk da cewar basa gaban kotun.
Sai dai lauyan wanda ake kara na 6 barrister Nuraini Jimo SAN ya yi suka inda ya bayyana cewar kotun ta dakata tun da sun daukaka kara ya kuma bayyana cewar kotun bata da hurumi sannan kunshin tuhume-tuhumen yana dauke ta kura-kurai.
Kotun zata bayyana matsayarta a yau da rana.
Tun da farko gwamnatin kano ta yi karar Ganduje da mutane 6 bisa zargin almundahana akan kudi sama da Naira Biliyan 4 da aka yi zargin sun sayarda wasu filaye sun raba kudin.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su