Connect with us

Siyasa

Zauren jam’iyyun haɗin kan kasa IPAC sun cire shugaban jam’iyyar LP na Kano Abdullahi Raji daga cikin tafiyar su 

Published

on

Sakataren zauren jam’iyyun haɗin kan kasar nan, IPAC na ƙasa reshen jihar Kano, kuma shugaban jam’iyyar APM na Kano Honarable Nuhu Idris, ya ce sun cire shugaban jam’iyyar LP na jihar Kano Abdullahi Raji daga cikin tafiyar su ta IPAC, baki ɗaya.

Sakataren na IPAC, Nuhu Idris ya ce sun dauki wannan mataki ne bisa yadda Rajin ke amfani da kungiyar CUPP, da rusassun jam’iyyun kasar nan suka samar a baya, a dan haka, duk wata jam’iyyar dake da rijista a yanzu na ƙarƙashin IPAC.

Ya kuma ce dokar da ta kafa IPAC, ba ta bai wa ɗan kowacce jam’iyya damar shiga hurumin wata jam’iyyar ba kamar yadda Rajin ke ƙoƙarin yi a rikicin dake faruwa a jam’iyyar APC a nan jihar Kano.

Shugaban jam’iyyar APM, ɗin Honarable Nuhu Idris, ya ce sun cire Rajin daga tafiyar ta IPAC ne, sakamakon wata sanarwa da ya fitar, ya ce, ka da hukumar zaɓe INEC, ta yi watsi da shugaban mazaɓar Ganduje, wanda hakan ba dai-dai ba ne a dokance, dan haka, suka fitar da shi daga cikin tafiyar tare da sanar da shugabancin jam’iyyar sa na kasa.

Hangen Dala

Lauyoyin gwamnatin Kano sun bukaci a kamo Ganduje

Published

on

Babbar kotun jaha mai lamba 7 karkashin jagorancin mai sharia Amina Adamu ta sanya karfe biyu da rabi na ranar yau dan bayyana matsayarta akan batun gurfanar da tsohon gwamnan kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa da wasu mutane.

A zaman kotun na yau lauyoyin gwamnatin jaha sun bayyana wa kotun cewa an sadar da sammace ga wadanda ake kara ta hanyar kafafen yada labarai kamar yadda kotun ta yi umarni tun a baya amma wadanda ake kara basu samu damar halartar kotun ba dan haka ya roki ko dai a kamo su ko kuma kotun ta ci gaba duk da cewar basa gaban kotun.

Sai dai lauyan wanda ake kara na 6 barrister Nuraini Jimo SAN ya yi suka inda ya bayyana cewar kotun ta dakata tun da sun daukaka kara ya kuma bayyana cewar kotun bata da hurumi sannan kunshin tuhume-tuhumen yana dauke ta kura-kurai.

Kotun zata bayyana matsayarta a yau da rana.

Tun da farko gwamnatin kano ta yi karar Ganduje da mutane 6 bisa zargin almundahana akan kudi sama da Naira Biliyan 4 da aka yi zargin sun sayarda wasu filaye sun raba kudin.

Continue Reading

Labarai

Da Dumi Dumi:- EL Rufai ya kai karar majalisar dokoki

Published

on

Tsohon Gwamna jahar Kaduna Mal. Nasir elrufai ya Maka majalisar Dokokin jahar Kaduna a gaban Kotu a bisa bata Masa Suna da majalisar tayi na cewa Gwamnatin sa ta sace kudaden jahar da Suka naura naira miliyan dubu Dari Hudu.

Tsohon Gwamna ya shigar da karar ce, a Gaban babbar kotun taraiyya dake NDA Kaduna a safiyar Laraban nan 26 ga watan Yuni 2024.

Inda ya bukaci Kotun data tursasa majalisar ta bashi hakuri a bainar jama’a, sakamakon Kazafin da Yan majalisan Suka yi masa da mukarraban Gwamnatinsa data gabata.

 

Karin bayani na nan tafe….

Continue Reading

Siyasa

Mun ƙudiri aniyar gyara tarbiyyar Matasa a jahar mu – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin Kano tasha alwashin ci gaba da magance matsalar tsaro musamman wajen kawo karshen kwacen waya da harkar Daba da ake fama dashi a jihar kano.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ne ya bayyana hakan a yayin karɓar baƙuncin mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero, a fadar fadar gwamnatin Kano, a wani ɓangare na bikin hawan Nassarawa, da ya gudana a yau Juma’a.

Abba Kabir, ya kuma ce duk da matsalolin da gwamnatin Kano ta fuskanta a baya na harkar shari’a, amma hakan bai hana ta cika alkawarin da ta ɗauka ga al’ummar jihar kano a yakin neman zaben shekarar 2023 da ta gabata ba.

Ya ƙara da cewa gwamnatinsa ba ta tsaya ba sai da ta yi kokarin magance matsalar da harkar Ilimi ke fama dashi wajen gyara makarantu da fitar da ɗalibai kasahen waje dan karo Ilimi kyauta.

“Gwamnatin mu ta bijiro da tsarin tallafawa masu harkar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da harkar Daba, da sana’oin dogaro da kai domin kawo karshen Daba a jihar kano, “in ji Gwamna Abba Kabir”.

Hawan Nasarawa dai hawa ne da ake sada zumunci a tsakanin masarautar Kano da gwamnatin Jihar Kano, da kuma al’ummar jihar, wanda da aka saba gudanar da shi a duk rana ta uku, na bikin ƙaramar Sallah, da Babba.

Da yake jawabi tunda farko mai martaba sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yabawa gwamnatin Kano akan tsarin da ta fito dashi na ciyar da al’ummar jihar kano gaba, musamman ma tsarin ciyarwar azumi da tayi ga mabukata a watan Ramadan da ya gabata.

Ya ci gaba da cewa, “Wannan ciyarwar ga al’umma tsari ne da ya kamata ya ɗore domin rage raɗaɗi da yunwa da ake fama da ita; muna shawartar Gwamnatin Kano, da ta saka ido sosai wajen kawo ƙarshen Daba da ƙwacen waya da hawa doki ana sukuwa ba bisa ka’ida ba, “in ji Sarkin”.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito mana cewa, Sarkin ya kumashawarci gwamnatin Kano, da ta ƙara dagewa wajen ci gaba da tallafawa Ilimin ɗalibai da ke fadin jihar kano, da sauran ayyuka da za su kawo wa jihar kano ci gaba.

Continue Reading

Trending