Manyan Labarai
Wasu ɓata gari sun raunata kwamandan Bijilante da wasu mutane da dama cikin wata unguwa a Kano

Wasu bata gari rike da muggan makamai, sun raunata mutane da dama, ciki har da kwamandan Bijilante na unguwar Gaida Goruba da ke ƙaramar hukumar Kumbotso a jihar Kano, Abdulmalik Isah.
Wasu mutane biyu da al’amarin ya rutsa dasu sun shaidawa wakilin Dala FM Kano, Abubakar Sabo cewa, matasan sun shiga cikin unguwar ta Gaida Goruba, ne a cikin daren jiya Alhamis, da misalin karfe 3, inda suka rinƙa saran mutane da muggan Makamai.
Al’amarin da ya jawo raunata mutane da dama wanda yanzu haka suna Asibiti suna karɓar magani, ciki kuwa har da kwamnadan ƙungiyar Bijilanten yankin Abdulmalik Isah.
Ita ma wata matashiya da aka Sassari mijin yayar ta, bayan da matasan suka ɓalle ƙofar gidan suka shiga, ta ce har yanzu mutumin bai san inda kansa ya ke ba.

Manyan Labarai
Hukumar Shari’a ta shirya kawo ƙarshen ƙwacen Waya a Kano

Hukumar Shari’a ta jihar Kano, ta ce za ta tunkari matsalar ƙwacen Waya haɗin gwiwa da dukkan shugabannin kasuwannin wayoyi da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro da hukunci a jihar Kano, don kawo ƙarshen matsalar.
Kwamishina na biyu a hukumar Shari’a ta jihar Kano, Sheikh Ali Ɗan Abba, ne ya bayyana hakan a shafin sa na sada zumunta a ranar Asabar, biyo bayan yadda ake ci gaba da fuskantar ƙalubalen ƙwacen waya a birnin Kano, lamarin da ke sanadiyyar rayukan jama’a daga masu ƙwacen wayar, tare da asarar dukiyoyi.
Sheikh Ali Ɗan Abba, ya kuma ce, a makon da za a shiga ne Hukumar shari’a ta jihar Kano, za ta bayyana irin tsauraran matakan da za ta ɗauka a kan wannan masifar da ta gallabi al’ummar jihar, wato matsalar fashin Waya da Makami.
Tashar Dala FM Kano, ta ruwaito cewa, Sheikh Ɗan Abba, ya kuma yi addu’a akan lamarin, inda ya ce “Allah ya taimake mu ya kawo mana ƙarshen wannan masifar ta fashin Waya da makami a Kano”.
Wannan dai na zuwa ne yayin da al’ummar Kano, da masana harkokin tsaro, ke ci gaba da kiraye-kiraye ga mahukunta da su ƙara tashi tsaye wajen yin abinda ya dace don kawo ƙarshen ƙwacen waya, da faɗan Daba, da kuma shaye-shayen kayan maye, a jihar, la’akari da yadda lamarin ya ke damun jama’a.

Baba Suda
NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.
Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.
A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.
Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Labarai
Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta
Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.
Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su