Connect with us

Manyan Labarai

Mun shiga damuwa kan kwashe motocin da suke aikin hanyar mu – Mazauna garin Kara Gwarzo a Kano

Published

on

Al’ummar garin Kara da ke karamar hukumar Gwarzo a jihar Kano, sun jaddada rokon su kan magance musu matsalar rashin ruwan Sha da ta karancin Likitoci a asibitin yankin su, da ta lalacewar ajujuwa a makarantu, da kuma ta lalacewar hanyar su, al’amarin da ke damun su.

A zantawar wakilin Dala FM, Hassan Mamuda Ya’u da sakataren kungiyar Matasa ta samar da ci gaban garin na Kara da ke karamar hukumar Gwarzo, Khalid Sale, ya ce a baya-bayan nan gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ya ƙaddamar da gyaran hanyar tasu, amma yanzu haka sun ga an kwashe motocin da suke aikin ba tare da sun san dalilin hakan ba.

Ya ci gaba da cewa, a don haka ne suke kira ga gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da dukkanin shugabannin yankin su, da su kai musu ɗaukin da ya dace dan magance musu matsalolin da suke addabar su.

“Tsayawar aikin gyara hanyar tamu da ta tashi daga bakin titin Gwarzo ta wuce zuwa unguwannin Kara, da Sabon layin Kara, ta wuce Ɗalangashi, har zuwa jihar Katsina, yanzu haka tayi matuƙar lalacewar da idan akayi ruwan sama muna shiga cikin Damuwa, “in ji Khalid”.

Ya kuma ƙara da cewa suna fama da matsalar rashin ruwan Sha, da ta ƙarancin Likitocin a Asibitin yankin su, da kuma ta lalacewar ajujuwa a makarantun su, amma ta lalacewar hanyar tafi yankin nasu tafi damun su.

A cewar sa, “Mun yi farin ciki da miƙa godiyar mu ga gwamnan Kano, bisa yadda ya ƙaddamar da gyara hanyar garin mu na Kara da ke ƙaramar hukumar Gwarzo, amma dai bamu ji daɗin kwashe motocin da akayi ba, domin yanzu haka aikin ya tsaya cak, “in ji shi”.

Akan al’amarin ne wakilin namu ya tuntubi shugaban riko na ƙaramar hukumar ta Gwarzo Mani Tsoho Zango, ta wayar tarho, sai dai a lokacin ya ce ya bashi lokaci kasancewar a lokacin da aka kirashin yana tsaka da wani uziri.

Idan ba’a manta ba al’ummar yankin sun daɗe da shaidawa Dala FM Kano, halin damuwar da suke cikin kan rashin al’amuran more rayuwa a yankin nasu.

Manyan Labarai

Wata Sabuwa: Lauya ya nemi kotu ta kama kwamishinan Shari’a na jihar Kano

Published

on

Wani lauya mai zaman kan sa a jihar Kano Barista Haruna Musa Muhammad, ya yi ƙorafi a gaban babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar, akan ta kama kwamishinan Shari’a na jihar Kano Barista Haruna Isah Dederi, da wasu manyan mukarraban gwamnatin jihar.

Lauyan wanda yake wakiltar mai kara Nura Bashir Ahmad, ya bayyana cewar gwamnatin jihar Kano ta rushe wa Nura gida duk da cewar ya samu hukunci a babbar kotun tarayya akan kada a rushe masa gidan.

Cikin wata ƙunshin Shari’a mai lamba FHC/KN/CS/240/2023, mai Shari’a Simon Amobida, ya ayyana cewar kotun tarayya ta gamsu da takardun mallaka da mai ƙara Bashir Ahmad ya gabatar mata, don haka ne ma ta ayyana cewar gidan mallakinsa ne.

Kotun dai tun a ranar 13 ga watan biyu na shekarar da ta gabata ta 2024, ta zartas da hukuncin akan batun.

Mai karar Bashir ta bakin lauyansa Barista Haruna Musa, sun bayyana cewar sun rubuta koke zuwa gaban kotun da ta yi hukuncin tun da dai suna zargin waɗanda ake ƙarar sun raina wannan hukunci kamar yadda ya bayyana a zantawar sa da wakilin Dala FM Kano.

Akan wannan batu ne wakilin namu ya tuntuɓi kwamishinan Shari’a na jihar Kano Barista Haruna Isah Dederi, ta wayar salula, sai dai bai samu damar ɗaa wayar ba, ya kuma aike masa da gajeren saƙon kar ta kwana nan ma bai bada amsa ba, amma yana dakon sa.

Continue Reading

Manyan Labarai

Budurwa ta mutu yayin wata Gobara da ta kama cikin gidan su a Kano

Published

on

Wata Gobara da ta tashi a wani gida ta yi sanadiyyar rasuwar wata budurwa a unguwar Ja’en Sabere da ke ƙaramar hukumar Gwale a Kano da ke arewacin Najeriya, tare da ƙonewar wasu sassan gidan.

Mamallakin gidan da lamarin ya faru mai suna Saminu Abba ne ya tabbatar wa tashar Dala FM faruwar lamarin a ranar Alhamis, 16 ga watan Janairun 2025.

Ya ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe ɗaya na daren jiya Laraba, lamarin da jami’an hukumar kashe Gobara ta jihar Kano da ma ƴan Bijilanten yankin da sauran al’umma suka kai ɗauki.

“Muna cikin Bacci muka ji wata ƙara da ihun mutanen unguwa, da muka tashi muka ga Gobara ce ta tashi a wasu sassan gidan mu kuma wutar ta tare hanyar da za mu fita gashi tana ci ba ƙaƙƙautawa, “in ji Saminu”.

Ya ci gaba da cewa, “Bayan jami’an hukumar kashe Gobara da ƴan Bijilanten yankin, da sauran al’umma sun kawo musu ɗauki, ne aka fasa Gini ta gidan maƙotan su inda su shida suka fita daga gidan sai dai ƴar su budurwa mai shekaru 18 mai lalurar Sikila ta rasu”.

Mallam Saminu Abba ya ƙara da cewa, kayayyakin su na sawa da wasu tarin kayayyaki da dama ne suka ƙone ƙurmus, lamarin da ya nemi ɗaukin mahukunta da su kai musu ɗauki bisa halin da suka samu kan su a ciki.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ba kan ta: An sace birkin jirgin sama guda 80 a Kano

Published

on

Kotun majistret mai lamba 70 da ke jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Faruk Ibrahim Umar, ta aike da wasu mutane gidan ajiya da gyaran hali bisa zargin su da haɗa baki da Sata.

Ƙunshin zargin da ake yi wa mutanen ya ayyana cewar, a ranar 11 ga watan 12 na shekarar da ta gabata ta 2025, wani mutum mai suna Otaru Bashir ma’aikaci a kamfanin sifirin jiragen sama na Azman, ya yi ƙorafi cewar mai gadin kamfanin nasu ya haɗa baki da wasu mutane sun sace musu birkin jirgin sama guda 80.

Ana dai zargin mutanen ne da sace waɗannan barakun wato birkin jirgin sama guda tamanin a filin jirgin tashi da saukar jiragen sama na Malam Aminu Kano.

Mutanen da ake zargin sun hadar da Nuhu Auwalu da Yakubu Bala da Emanuel Luka, sai kuma safiyanu Abdullahi.

Ko da aka karanta wa mutanen ƙunshin zargin da ake yi musu dukkaninsu sun musanta, a nan ne kotun ta aike da mutanen gidan gyaran hali tare da sanya ranar 11 ga watan gobe dan sauraron shaidu akan shari’ar.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewar, yayin zaman kotun an ambata cewar, binciken ƴan sanda ya bayyana cewar kimar kayan ya kama Naira miliyan dari da arba’in, sai dai yayin bincike an gano birkin jirgin guda uku a hannun wanda ake zargi na uku mai suna Yakubu Bala.

Continue Reading

Trending