Connect with us

Manyan Labarai

Mun shiga damuwa kan kwashe motocin da suke aikin hanyar mu – Mazauna garin Kara Gwarzo a Kano

Published

on

Al’ummar garin Kara da ke karamar hukumar Gwarzo a jihar Kano, sun jaddada rokon su kan magance musu matsalar rashin ruwan Sha da ta karancin Likitoci a asibitin yankin su, da ta lalacewar ajujuwa a makarantu, da kuma ta lalacewar hanyar su, al’amarin da ke damun su.

A zantawar wakilin Dala FM, Hassan Mamuda Ya’u da sakataren kungiyar Matasa ta samar da ci gaban garin na Kara da ke karamar hukumar Gwarzo, Khalid Sale, ya ce a baya-bayan nan gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ya ƙaddamar da gyaran hanyar tasu, amma yanzu haka sun ga an kwashe motocin da suke aikin ba tare da sun san dalilin hakan ba.

Ya ci gaba da cewa, a don haka ne suke kira ga gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da dukkanin shugabannin yankin su, da su kai musu ɗaukin da ya dace dan magance musu matsalolin da suke addabar su.

“Tsayawar aikin gyara hanyar tamu da ta tashi daga bakin titin Gwarzo ta wuce zuwa unguwannin Kara, da Sabon layin Kara, ta wuce Ɗalangashi, har zuwa jihar Katsina, yanzu haka tayi matuƙar lalacewar da idan akayi ruwan sama muna shiga cikin Damuwa, “in ji Khalid”.

Ya kuma ƙara da cewa suna fama da matsalar rashin ruwan Sha, da ta ƙarancin Likitocin a Asibitin yankin su, da kuma ta lalacewar ajujuwa a makarantun su, amma ta lalacewar hanyar tafi yankin nasu tafi damun su.

A cewar sa, “Mun yi farin ciki da miƙa godiyar mu ga gwamnan Kano, bisa yadda ya ƙaddamar da gyara hanyar garin mu na Kara da ke ƙaramar hukumar Gwarzo, amma dai bamu ji daɗin kwashe motocin da akayi ba, domin yanzu haka aikin ya tsaya cak, “in ji shi”.

Akan al’amarin ne wakilin namu ya tuntubi shugaban riko na ƙaramar hukumar ta Gwarzo Mani Tsoho Zango, ta wayar tarho, sai dai a lokacin ya ce ya bashi lokaci kasancewar a lokacin da aka kirashin yana tsaka da wani uziri.

Idan ba’a manta ba al’ummar yankin sun daɗe da shaidawa Dala FM Kano, halin damuwar da suke cikin kan rashin al’amuran more rayuwa a yankin nasu.

Manyan Labarai

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren gwamnatin Kano da wani Kwamishina

Published

on

Jam’iyyar NNPP ta jihar Kano ta bayyana dakatar da sakataren gwamnatin jihar Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da Kwamishinan Sufuri na jihar Kano Muhammad Diggwal, daga cikin jam’iyyar.

Shugaban jam’iyyar NNPP a Kano Dakta Hashim Sulaiman Dungurawa ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a cikin daren yau Litinin.

Hashim Dungurawa, ya ce dakatar da ƙusoshin gwamnatin jihar Kano su biyu ya biyo bayan zargin keta alfarmar jagoranci, da ta Jam’iyya, da kuma keta alfarmar gwamnati, a don haka ne suka ɗauki matakin ba tare da yin wasa ba akai.

“Jagorancin shugabancin jam’iyyar mu na ƙananan hukumomin da mutane biyun suka fito sun gabatar mana da ƙorafe-ƙorafe kan ƙusoshin gwamnatin biyu, akan zarge-zarge da ake musu ya sa muka ɗauki matakin dakatar da su, har sai mun gama bincike, “in ji Dungurawa”.

Sulaiman ya ƙara da cewar dakatar da Abdullahi Baffa Bichi da Muhammad Diggwal ta fara aiki ne daga ranar Litinin 14 ga watan Oktoban 2024, kamar yadda jam’iyyar ta samu ingantattun shawarwari akan zargin da ake musu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ku tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa na Ɗorayi bisa halin da suke ciki – Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam 

Published

on

Ƙungiyar wayar da kan jama’a da kare haƙƙin ɗan adam da tallafawa mabuƙata, ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, ta tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa da ke unguwar Ɗorayi, da dafaffen abinci, domin rage musu wata damuwa.

Ƙungiyar dai ta rabawa masu lalurar Ƙwaƙwalwar abincin ne da yammacin Asabar 12 ga watan Oktoban 2024, tare da ziyartar wata makarantar tsangaya da ke unguwar Ɗorayi, inda ɗalibai 1,000 suka rabauta da tallafin dafaffen abincin.

Da yake yiwa Dala FM Kano, ƙarin bayani daraktan ƙungiyar ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, Kwamared Auwal Usman, ya ce rahotannin da suka samu kan yadda mazauna Asibitin da kuma makarantun tsangayar ke fuskantar ƙalubalen abinci ya sa suka kai musu tallafin domin rage musu wani raɗaɗi.

 

Wasu daga cikin masu lalurar Ƙwaƙwalwar da suka fara samun sauƙi, sun nemi ɗaukin gwamnatin jihar Kano wajen magance ƙalubalen da suke fuskanta na rashin kyawun wuraren da suke kwana da sauran matsaloli, ko sa samu wani sauƙi.

Da yake nasa jawabin mai kula da Asibitin da ake kula da masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi a Kano, Munnir Ɗahiru Kurawa, ya miƙa godiyar sa ga tawagar ƙungiyar bisa kaɓakin alkhairin da ta saukewa masu taɓin hankalin.

Wannan dai na zuwa ne makwanni kaɗan da gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ziyarci Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi, har ma ya bada umarnin aje a gyara shi, sai dai kawo yanzu hakan bata samu ba kamar yadda wata majiya ta bayyana.

Continue Reading

Manyan Labarai

Mun biya wa mazauna gidan gyaran hali tara don rage musu raɗaɗi a Kano – Human Right

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Right Network, ta biya wa wasu mazauna gidan ajiya da gyaran hali na Goron da na yara da ke Kano, su 10 tara, waɗanda suka shaƙi iskar ƴanci.

Shugaban gudanarwar ƙungiyar na ƙasa Kwamared Tasi’u Idris Idris (Soja) ne ya bayyana wa manema labarai hakan jim kaɗan da fitowar su daga gidan gyaran halin lokacin da mutanen suka shaƙi iskar ƴanci a ranar Alhamis.

Tasi’u Idris ya ce sun ɗauki matakin biya wa mutanen tarar ne ciki har da Matasa domin su shaƙi iskar ƴanci kamar kowa, duba da halin matsin rayuwar da ake ciki yanzu a ƙasar nan.

Kasancewar guda daga cikin mambobin ƙungiyar ne na ƙaramar hukumar Kura mai suna Usman Yusuf Gun-Dutse, haɗin gwiwa da uwar ƙungiyar ta ƙasa ne suka biya tarar, a don haka ne muka zanta da shi, inda ya ce ya yi hakan ne domin taimaka wa mutanen.

Da yake nasa jawabin akan batun mai magana da yawun gidajen gyaran halin na jihar Kano SC Musbahu Lawan Ƙofar Nassarawa, ya ce abinda ƙungiyar ta yi abin jin daɗi ne bisa yadda aka rage cunkoson mutane a gidajen.

Majiyar tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewar, tuni dai mutanen suka koma cikin ƴan uwan su domin ci gaba da gudanar da harkokin su na yau da kullum.

Continue Reading

Trending