Manyan Labarai
Mun shiga damuwa kan kwashe motocin da suke aikin hanyar mu – Mazauna garin Kara Gwarzo a Kano
Al’ummar garin Kara da ke karamar hukumar Gwarzo a jihar Kano, sun jaddada rokon su kan magance musu matsalar rashin ruwan Sha da ta karancin Likitoci a asibitin yankin su, da ta lalacewar ajujuwa a makarantu, da kuma ta lalacewar hanyar su, al’amarin da ke damun su.
A zantawar wakilin Dala FM, Hassan Mamuda Ya’u da sakataren kungiyar Matasa ta samar da ci gaban garin na Kara da ke karamar hukumar Gwarzo, Khalid Sale, ya ce a baya-bayan nan gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ya ƙaddamar da gyaran hanyar tasu, amma yanzu haka sun ga an kwashe motocin da suke aikin ba tare da sun san dalilin hakan ba.
Ya ci gaba da cewa, a don haka ne suke kira ga gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da dukkanin shugabannin yankin su, da su kai musu ɗaukin da ya dace dan magance musu matsalolin da suke addabar su.
“Tsayawar aikin gyara hanyar tamu da ta tashi daga bakin titin Gwarzo ta wuce zuwa unguwannin Kara, da Sabon layin Kara, ta wuce Ɗalangashi, har zuwa jihar Katsina, yanzu haka tayi matuƙar lalacewar da idan akayi ruwan sama muna shiga cikin Damuwa, “in ji Khalid”.
Ya kuma ƙara da cewa suna fama da matsalar rashin ruwan Sha, da ta ƙarancin Likitocin a Asibitin yankin su, da kuma ta lalacewar ajujuwa a makarantun su, amma ta lalacewar hanyar tafi yankin nasu tafi damun su.
A cewar sa, “Mun yi farin ciki da miƙa godiyar mu ga gwamnan Kano, bisa yadda ya ƙaddamar da gyara hanyar garin mu na Kara da ke ƙaramar hukumar Gwarzo, amma dai bamu ji daɗin kwashe motocin da akayi ba, domin yanzu haka aikin ya tsaya cak, “in ji shi”.
Akan al’amarin ne wakilin namu ya tuntubi shugaban riko na ƙaramar hukumar ta Gwarzo Mani Tsoho Zango, ta wayar tarho, sai dai a lokacin ya ce ya bashi lokaci kasancewar a lokacin da aka kirashin yana tsaka da wani uziri.
Idan ba’a manta ba al’ummar yankin sun daɗe da shaidawa Dala FM Kano, halin damuwar da suke cikin kan rashin al’amuran more rayuwa a yankin nasu.
Manyan Labarai
Gundura da ake zargi da sarewa Ɗan Bijilante hannu da fasa motar ƴan sanda ya shiga hannu
Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta samu nasarar cafke wani Matashi mai suna Inuwa Zakari ɗan shekara 24, wanda akafi sani da Gundura, wanda ake zargi da sarewa wani Ɗan Bijilante hannu, da kuma fasa motar Ƴan Sanda, da wasu Laifuka
Kakakin rundunar ƴan sandan SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar da ya aikowa Dala FM a daren Litinin, Kiyawa ya ce Matashi Gundura sun daɗe suna neman sa ruwa a jallo bisa zargin sa da tarin Laifuka.
“Gundura ya kasance abokin fitaccen ɗan Dabar nan Abba Burakita ɗa unguwar Ɗorayi da ya rasu a baya, kuma har kotu ma muka gurfanar da shi daga baya ya fita amma bai dai na abinda ya ke yi ba, a ranar zaɓen ƙananan hukumomin Kano, da ya shigo yana yunƙurin tayar da hankalin al’umma jami’an mu suka kama shi, “in ji SP Kiyawa”.
Har ila yau, Abdullahi ya ce an kama Gundura da wukake guda biyu a wani waje na matattarar Yan Daba da suke kira “Jungle” a Unguwar Dorayi.
Rundunar ƴan sandan ta ce ta kuma cafke ƙarin wasu matasa 14, da ake zargin su da aikata maban-banta laifuka, inda aka kama su a tsakanin 25 ga zuwa 27 na watan Oktoban 2024.
SP Kiyawa ya ƙara da cewa yanzu haka waɗanda ake zargin ana ci gaba da bincike a kan su a babban sashin binciken manyan laifuka na CID, da ke hedikwatar rundunar da ke Bompai a Kano, kuma da zarar an kammala za’a gurfanar da su a gaban kotu.
Manyan Labarai
Ku zauna lafiya yayin zaɓen ƙananan hukumomin da ake gudanarwa a Kano – Kwankwaso
Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi kira ga al’umma da su tabbatar da an samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a zaɓen ƙananan hukumomin da ake gudanarwa yau a Kano.
Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kaɗa ƙuri’a a mazaɓar sa ta Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a Kano.
Ya kuma ce akwai buƙatar al’ummar jihar su fita rumfunan zaɓen su kaɗa ƙuri’un su domin ƙara inganta Demukuraɗiyya a jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.
Kwankwaso ya kuma jaddada wa al’ummar jihar cewar gwamnatin Kano za ta ci gaba da ayyukan alheri a faɗin jihar, domin samar da ci gaban Jama’a.
A ranar Asabar ɗin nan ne dai ake gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar Kano 44, wanda shugabannin fa za’a zaɓa za su shafe tsawon shekaru uku-uku a karagar mulki.
Kafin wannan rana an dai samu cece-kuce akan batun zaɓen, wanda a ranar Talatar da ta gabata wata babbar kotun tarayya da ke jihar Kano, ta dakatar da shugabancin hukumar zaɓen ta jihar Kanseic, da umartar Ƴan sandan jihar su ƙairacewa shiga aikin zaɓen.
Ko da dai a jiya Juma’a babbar kotun jahar Kano ƙarƙashin mai Shari’a Sunusi Ado Ma’aji, ta umarci hukumar zaɓen ta gudanar da zaɓen a yau Asabar, tare da umartar Ƴan sandan su shiga aikin zaɓen, ko da dai wasu mazauna jihar sun shaidawa Dala FM cewar, ba su ga jami’an ƴan sanda ba a wuraren zaɓen.
Jami’an tsaron da aka gani sun haɗar da ƴan Karota, da na Hisbah, da kuma ƴan Bijilante, da jami’an rundunar tsaro da ke yaƙi da ƙwacen Waya da faɗan Daba da magance Shaye-shaye ta Anty Snaching Phone da ke Kano.
Manyan Labarai
Har yanzu jam’iyyu 6 ne suka cika ƙa’idar zaɓen ƙananan hukumomin da za a gudanar kuma babu APC a ciki – KANSEIC
Hukumar zaɓe ta jihar Kano (KANSIEC), ta bayyana sunayen jam’iyyu 6 a matsayin waɗanda suka cika ƙa’idar shiga zaben ƙananan hukumomin da za a gudanar ranar Asabar a Kano.
Shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Malumfashi ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan babbar kotun jaha ta tabbatar da halaccin hukumar zaben.
Farfesa Malumfashi ya bayyana cewar jam’iyyun da suka cika ƙa’idar sun haɗar da Jam’iyyar AA, AAC, Accord, ADC, da APM da kuma jam’iyyar NNPP mai mulki a jihar Kano.
Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, shugaban hukumar zaben ya bukaci hukumomin tsaro da su fito su kare rayuka da dukiyoyin al’umma a lokacin gudanar da zaben, kamar yadda babbar kotun jaha ta umarce su a hukuncin da ta yi da ranar Juma’a 25 ga watan Oktoban 2024.
A ranar Alhamis dai an jiyo yadda kwamoshina mai kula da harkokin yaɗa labarai da al’amuran Shari’a na hukumar zaɓe ta jihar Kano Kanseic, Lawan Badamasi, ya ce za su yi amfani da jami’an tsaron cikin gida domin samar da tsaro yayin zaɓen.
Ya ci gaba da cewa daga cikin jami’an tsaron cikin gidan akwai irin su ƴan Karota, da na Hisbah, da kuma Ƴan Bijilante, domin samar da tsaro idan ƴan sanda suka ƙauracewa shiga aikin zaɓen kamar yadda suka samu umarnin hakan daga wata babbar kotun tarayya da ke jihar Kano.
-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su