Manyan Labarai
Mun sauya salon Zanga-zangar tsadar rayuwar da muka shirya gudanar wa a Kano – War Against Injustice

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam da yaƙi da rashin adalci da kuma bibiyar al’amuran da suka shafi shugabanci na gari, ta War Against Injustices, ta ce yanzu haka ta sauya salon gudanar da zanga-zangar lumanar tsadar rayuwa, daga fita kan titi zuwa shirya taron manema labarai da masu ruwa da tsakin ƙungiyar.
Daraktan ƙungiyar a nan Kano Kwamared Umar Ibrahim Umar, ne ya bayyana hakan a zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Litinin 29 ga watan Yulin 2024.
Ya ce, sun yanke shawarar shirya taron manema labarai ne su sanar da gwamnati, da sauran shugabanni halin matsin rayuwar da al’umma suka samu kan su a ciki, bisa yadda suka samu bayanan sirri kan yadda wasu ke yunƙurin amfani da zanga-zangar wajen tada hankalin al’umma, da kuma rufar wa kadarorin gwamnati.
“Abinda ya sa muka ce ba zamu yi zanga-zangar tsadar rayuwar a kan tituna ba saboda mu banbanta kan mu daga ɓata garin da suke yunƙurin tayar da hankalin al’umma wajen ƙone-ƙone da farwa kayayyakin gwamnati da na al’umma, “in ji shi”.
Kwamared Umar Ibrahim, ya ƙara da cewa burin su shine gwamnatin tarayya ta dawo da tallafin man Fetur, da cire ƙarin kuɗin wutar lantarkin da aka yiwa ƴan Najeriya, da kuma rage kuɗin karatun Ɗaliban jami’o’i, da matsalar tsaro, tare da sauƙaƙa wa al’ummar ƙasa.
“Dokar ƙasa sashi na 39, da na 40, ya bai wa kowanne ɗan ƙasa damar gudanar da zanga-zangar lumana, domin sanar da gwamnati damuwar su, a don haka ne ma muka ƙudirin aniyar gudanar da zanga-zangar a baya, amma saboda gujewa kai din ɓata gari, ya sa muka sauya salon ta zuwa taron manema labarai, “in ji kwamared Umar”.
Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya ruwaito cewa, kwamared Umar Ibrahim ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta samar da tsaro ga al’umma, da dai-dai al’amura domin ganin al’ummar Najeriya sun samu sauƙi.
Idan za’a iya tunawa wasu dandazon matsa sun ƙudiri gudanar da zanga-zangar lumana ne daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Yulin 2024, domin nusartar da gwamnatin tarayya halin matsin rayuwar da aka samu kai yanzu a ciki, dan ganin an magance matsalolin al’umma su samu sauƙi.

Manyan Labarai
Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.
Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.
Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.
A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.
Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Manyan Labarai
Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.
Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.
“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.
Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.
Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.
Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.
Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

Manyan Labarai
Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.
Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a
“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.
Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.
Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su