Connect with us

Labarai

Sanar da gwamnati ƙuncin rayuwar da ake ciki ta shafukan sada zumunta yafifita zanga-zanga – Human Rights

Published

on

Shugaban ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Sustainable Growth Initiatives for Human Rights Deplolopment ta kasa, kwamared Abubakar Musa Abdullahi, ya ce mai-makon masu shirya zanga- zangar tsadar rayuwa su fito kan tituna da kwalaye ko kuma riƙe Makami, yafi dacewa su mayar da hankali kan rubuce-rubuce a shafukan sada zumunta, domin nusar da gwamnati damuwar su.

Daraktan kungiyar a nan Kano Kwamared Abubakar Musa Abdullahi ne ya bayyana hakan yayin zantwar sa da gidan rediyon Dala FM Kano, a ranar Talata,

Ya ce gujewa hawa kan titunan yayin zanga-zangar tsadar rayuwar ka iya taimakawa wajen gujewa lalata kadarorin gwamnati da ma dukiyoyin al’umma.

Da yake nasa jawabin mai magana da yawun kungiyar sintirin Bijilante ta jihar Kano Usman Muhammad Ɗan-daji shawartar matasa ya yi, da su guji daukar makamai ko kuma karya doka yayin zanga-zangar lumanar da ake shirin gudanarwa, domin gujewa yin dana sani wanda ka iya janyo musu faɗawa hannun jami’an tsaro.

“Ƙungiyar mu ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, yanzu haka ta shirya tsaf wajen baza jamai’an mu a lungu da sakunan Kano, domin samar da tsaro a tsakanin al’umma, musamman a lokutan zanga-zangar, “in ji Ɗan-daji”.

Wannan dai na zuwa ne yayin da wasu mutane musamman ma Matasa suka shirya gudanar da zanga-zangar lumana akan tsadar rayuwar da aka samu kai a ciki, bayan da suka sanya ranar 1 zuwa 10 ga watan Augusta mai kamawa, domin gudanar da ita don sanar da gwamnatin tarayya halin matsin rayuwar da ake ciki.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending