Connect with us

Labarai

Hukumar gidajen gyaran hali ta Kano ta gargaɗi ƴan Film ɗin da suke nuni da cin mutumcin ta

Published

on

Hukumar da ke kula da gidajen gyaran hali na jihar Kano, ta ce ba za ta lamunci yadda wasu masu shirya Fina-finai suke amfani da kayan ta ko kuma wani ɓangare nata ba, kuma ba tare da ambasu umarni ba, wanda a wasu lokutan suke nuni da ɓatanci ga hukumar.

Mai magana da yawun hukumar SC Musbahu Lawan Ƙofar Nassarawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa gidan rediyon Dala FM, a ranar Laraba 31 ga watan Yulin 2024.

Ya ce ko kusa ko alama ba za su zuba idanu kan yadda wasu masu shirya Fina-finai suke amfani da kakin ta ko kuma wani ɓangare na gidajen ana cin mutumcin ta ba, yana mai cewa zasu rinƙa ɗaukar mataki akan irin hakan.

“Dukkanin waɗanda za su yi amfani da kayan hukumar mu ko kuma wani ɓangaren mu su rinƙa tuntuɓar mu, domin basu ƙa’idojin dokar hukumar, domin gujewa abinda ka iya zuwa ya dawo, “in ji SC Musbahu”.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya ruwaito cewa, SC Musbahu Lawan Ƙofar Nassarawa, ya kuma miƙa godiyar su ga al’umma bisa yadda suke bata haɗin kai tare da tallafawa mazauna gidajen gyaran halin.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending