Connect with us

Labarai

Alhazan Najeriya 30 ne suka rasu a aikin hajjin 2024 – NAHCON

Published

on

Hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON, ta tabbatar da cewa kimanin Alhazan Najeriya 30, ne suka rasu a lokacin gudanar da ibadar aikin Hajjin da ya gagabata na shekarar 2024.

Shugaban hukumar Malam Jalal Ahmad Arabi, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a birnin tarayya Abuja.

Ya kuma ce wasu Alhazan Najeriya biyar sun rasu ne saboda tsananin zafin ranar da akeyi a kasar Saudi Arebia, a yayin da sauran Alhazan Najeriya suka rasu a dalilin rashin lafiya daban-daban.

Jalal Arabi ya kara da cewa babbar matsalar da suka fuskanta a lokacin gudanar da ibadar aikin Hajjin da ya gabata, bai wuce matsalar tashin farashin Dalar Amurka ba, wanda hakan yasa farashin kuɗin kujerar aikin Hajjin da ya gabata yayi tashin gauron zabi.

Shugaban na NAHCON, Malam Jalal Arabi ya kuma yabawa gwamnatin shugaba Tunibu bisa irin yadda ya yi ƙoƙari wajen tallafawa Alhazan Najeriya.

Hukumomin kasar Saudi Arebia sun ce sama da Alhazai dubu daya da dari biyar ne suka rasu a aikin Hajjin da ya gabata a fadin duniya, wasu saboda zafin rana wasu kuma saboda rashin lafiya a yayin da wasu kuma sun rasu ne ta hanyar haɗarin ruguzowar gini a ƙasar.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending