Connect with us

Manyan Labarai

Zamu maka hukumar zaɓe ta Kano a kotu idan bata rage kuɗin tsayawa takarar shugabancin ƙaramar hukuma da na Kansila ba – Jam’iyyar PRP a Kano

Published

on

Jam’iyyar PRP ta jihar Kano ta tasha alwashin maka hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano, a kotu, matuƙar bata rage kuɗin da ta sanya a matsayin kuɗin tsayawa takarar shugabancin ƙaramar hukuma, da kuma na takarar Kansiloli, yayin da zaɓen ƙananan hukumomin ƙe ƙara gabatowa.

Shugaban hukumar zaɓen na jihar Kano Farfesa Sani Lawan Malumfashi, ne dai ya sanar da Naira miliyan goma a matsayin kuɗin tsayawa takarar shugabancin ƙaramar hukuma, yayin da ya ce masu neman takarar Kansila kuma za su biya Naira miliyan biyar-biyar.

Sakataren jam’iyar PRP, a jihar Kano Alhaji Musa Mai gari, shine ya bayyana shirin jam’iyyar kan ɗaukar matakin, yayin zantawar da gidan rediyon Dala FM, jim kaɗan da kammala taron da hukumar zaɓen ta gudanar yau a ofishinta, tare da masu ruwa da tsaki na jam’iyyu da ƙungiyoyin al’umma, inda ta kaddamar da jadawalin zaɓen ƙananan hukumomi da ka’idodi, tare da bayyana kuɗin Form ɗin tsayawa takarar.

A cewar sa, “Matuƙar hukumar zaɓen ba ta rage kuɗin Form, ɗin ba za mu garzaya kotu, duba da yadda kuɗaɗen da hukumar ta sanya sun yi yawan gaske bisa halin tsadar rayuwar da ake ciki “in ji Musa mai-gari”.

Shugabannin jam’iyyu da dama da ƴan takarakari ne dai ke ci gaba da nuna damuwar su kan yadda kuɗaɗen suka yi musu yawa.

Hukumar zaɓen mai zaman kanta ta jihar KANSEIC, ta sanya ranar 30 ga watan Nuwamban shekarar 2024, a matsayin ranar da za’a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi 44 da suke faɗin jihar Kano.

Hukumar ta kuma ce duk wanda zai tsaya takarar shugabancin ƙaramar hukuma, sai ya kai shekara 30 zuwa dama, yayin da shekarun ƴan takarar Kansila kuma zasu fara daga shekaru 25 zuwa sama.

Manyan Labarai

Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Published

on

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.

Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a

“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.

Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.

Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Continue Reading

Manyan Labarai

An ga watan ƙaramar Sallah a Najeriya – Sarkin Musulmi

Published

on

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na uku ya tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya, inda za a yi karamar Sallah gobe Lahadi.

Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a yayin jawabin da ya gabatar a cikin daren Asabar ɗin nan, ya ce sun samu rahotannin ganin watan ne daga sassa daban-daban na ƙasar nan.

Alhaji Sa’ad Abubakar ya ce daga cikin guraren da aiko musu da ganin jinjirin watan na Shawwal akwai Zazzau, da kuma daga Sarkin Dutse, da Arugungu, da kuma Shehun Borno, da dai sauran gurare daban-daban na Najeriya.

Ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su gabatar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali, tare da taimaka wa mabuƙata.

Tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewa, biyo bayan sanarwar fadar mai alfarma Sarkin Musulmi, ya kasance ranar Lahadi take 1 ga watan Shawwal na shekarar 1446, wato ranar ƙaramar Sallah.

Continue Reading

Manyan Labarai

Shugaba Tinubu da Sifeton Ƴan Sanda ku bi wa mutanen mu da aka yi wa kisan gilla hakƙin su – Rt. Hon. Rurum

Published

on

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Rabo, Kibiya da Bunkure, Kabiru Alhassan Rurum, ya bayyana kaɗuwar sa bisa kisan gillan da aka yi wa wasu Mafarauta su kusan 16, a garin Uromi da ke jihar Edo, a lokacin da suke hanyar su ta komawa Kano daga jihar Rivers.

Honarable Kabiru Rurum, ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da aka aikowa Dala FM Kano a ranar Asabar, ya ce daga cikin mutanen da aka ƙona akwai mutum 11 da suka fito daga mazaɓun yankin sa na Kibiya da Bunkure, inda wasu 6 suka samu muggan raunuka suna karɓar Magani yanzu haka a jihar Edo.

A cewar Ɗan Majalisar, “Wannan abu da matasan garin Uromi a jihar Edo, suka yi ya saɓa da dokar kasa, kuma mummunan laifi ne, a don haka za mu bi kadin hakƙin mutanen mu da aka kashe a kuma waɗanda aka jikkata, “in ji shi“.

Kabiru Rurum, ya ce a matsayinsa na wakilin mutanen da aka kashe a majalisar Wakilai ta ƙasa, yana kira ga shugaban Najeriya Bola Tinubu, da babban Sifeton ƴan sanda, da su yi duk mai yiyuwa wajen ganin an kamo waɗanda suka yi wannan aika-aikar tare da hukunta su, da kuma biyan diyya ga iyalan waɗanda suka rasu da kula da waɗanda suka jikkata.

“Kasancewar wannan bashi ne na farko da ake samun wasu ɓata gari na tare matafiya akan hanya da basu ji ba basu gani ba su kashe su, a don haka muna fatan wannan karon gwamnati da sauran hukumomin tsaro za su ƙaddamar da ƙwaƙƙwaran bincike don ɗaukae mataki kamar yadda dokar kasa ta tanada, “in ji Rurum”.

Ɗan majalisar ya kuma jajantawa dukkanin al’ummar jihar Kano musamman Iyalan waɗanda suka rasu, tare da addu’ar Allah ya gafarta musu yasa Jannatul Firdausi makomar su, su kuma waɗanda suka jikkata Allah ya basu lafiya.

Continue Reading

Trending