Connect with us

Manyan Labarai

An kama mutumin da ake zargi da damfarar wasu mata wajen karɓar musu kuɗaɗe da zummar zai samar musu aiki a Kano

Published

on

Rundunar tsaro ta Civil Defense a nan Kano ta kama wani mutum da zargin laifin damfarar wasu mata wajen karɓar kudadensu da sunan zai samar musu aiki a wasu hukumomin gwamnati da na tsaro.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar SC Ibrahim Idris Abdullahi ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya aikowa Dala FM a ranar Laraba.

Ya ce mutumin mai suna Mu’azu Muhammad Ibrahim, da ke unguwar Sagagi sun kamashi ne sakamakon korafe – korafen da suka samu daga wasu mata da suka bayyana musu cewa, ya karbi kudinsu sama da Naira miliyan ɗaya da dubu dari ɗaya da sunan zai nemar musu aiki, duk da bashi da damar hakan.

“A lokacin da jami’an mu suka binciki mutumin ya shaida musu cewa tabbas ya karɓi wadannan kuɗaɗen a wajen matan da summar zai samar musu aikin amma kuma al’amarin ƙarya ne bashi da takardun samar da aiki ko hanyar su, “in ji SC Ibrahim”.

SC Ibrahim ya kuma ƙara da cewa da zarar rundunar ta kammala binciken ta akan wanda ake zargi zata gurfanar dashi a gaban Kotu.

Da yake nasa jawabin mutumin da ake zargin mai suna Mu’az Muhammad Ibrahim, ya tabbatar da karɓar kuɗaɗen sai dai ya ce wasu kuɗaɗen suna hannun wata mata, amma dai ya yi nadama ba zai ƙara ba.

“Aƙalla watanni shida ke nan da fara bayar da kuɗaɗen nasu, abinda muka yi ba dai-dai ba ne kuma muna neman afuwa akai ba zamu sake ba, “in ji mutumin”.

Rundunar Civil Defense ɗin a jihar Kano, ta kuma ja hankalin al’umma da su rinƙa yin taka-tsantan tare da lura da irin mutanen da suka ce za su samar musu aiki, domin gujewa faɗawa komar ɓata gari.

Baba Suda

Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.

 

Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.

 

Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Continue Reading

Manyan Labarai

Da Ɗumi-Ɗumi! Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakin sa da ƴan majalisar jihar na watanni 6.

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.

Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani taƙaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.

Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin ƴan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan, tare da sanya dokar ta ɓaci a jihar.

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya daɗe da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saƙa tsakanin sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Continue Reading

Manyan Labarai

Isra’ila ta kashe sama da mutane 200 bayan karya yarjejeniyar tsagaita Wuta a Gaza

Published

on

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, tare da ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasdinawa.

Jaridar TRT Hausa ta ruwaito cewa, aƙalla Isra’ila ta kashe fiye da mutum 200 tare da jikkata ɗaruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti, kamar yadda majiyoyin wani asibiti a yankin Gaza suka bayyana.

Continue Reading

Trending