Connect with us

Manyan Labarai

Kwana biyu ya rage mu maka jam’iyyar NNPP a Kotu bisa zargin ƙin adalci yayin fidda ƴan takara a Kano – Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam da wayar da kan jama’a, ta Awareness for Human Right and Charity Foundation ta sha alwashin maka jam’iyyar NNPP ta jihar Kano, a kotu, matuƙar ba’a samu masalaha ba kan ƙorafin da suka samu na zargin da wasu masu sha’awar tsayawa takarar Kansila a mazaɓar Ɗandago da Sani Mai Nagge da ke ƙaramar hukumar Gwale suka yi kan take musu haƙƙi wajen tsayar da ƴan takara a mazaɓun nasu.

Daraktan ƙungiyar a matakin ƙasa Kwamared Auwal Usman Awareness ne ya bayyana hakan, yayin wani taron manema labarai da ƙungiyar ta gudanar ranar Laraba a ofishinta.

Wannan na zuwa ne bayan da mai neman tsayawa takarar Kansila a mazaɓar Ɗandago Hadi Shehu Abubakar, da wasu ƴan takarar Kansila a mazaɓar Sani Mai Nagge su biyu wato Mahfouz Musa da Musa Muhammad, dukka a ƙaramar hukumar Gwale, suka shigar da ƙorafin su a ofishin ƙungiyar.

Masu ƙarar sun zargi cewar jam’iyyar ta NNPP ba ta yi musu adalci ba wajen mayar da su saniyar ware, wajen tsayar da ƴan takarar a mazaɓun nasu.

Kwamared Auwal Awareness, ya kuma ce tun bayan da suka karɓi ƙorafin ne suka rubutawa jam’iyyar takarda mai ɗauke da wa’adin kwanaki biyar kan tayi abinda ya dace ko kuma su gauraya a gaban kotu, wanda ya ce yanzu haka wa’adin nasu ya rage kwanaki biyu.

Da yake jawabi tun da farko tsohon ɗan takarar kansilan a mazaɓar Ɗandago Hadi Shehu Abubakar, amadadin sauran masu ƙorafin ya ce, an umarce su ne da suje su yi sulhu akan tsayar da ƴan takarar a baya, amma bayan sun tafi sai sukaji an sanar da ƴan takarar a mazaɓun nasu, a don haka ne suka yi duk mai yiyuwa amma jam’iyyar ta NNPP ba ta yi komai ba, hakan yasa suka shigar da ƙorafin nasu a ofishin ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ɗin.

Akan wannan ƙorafi ne muka tuntuɓi shugaban jam’iyar NNPP ta jihar Kano, Dakta Hashim Sulaiman Dungurawa ta wayar tarho, wanda ya musanta zargin da tsofaffin ƴan takarar suka yi, inda ya ce damar su ɗaya ce idan ba’a yi musu adalci ba su canza jam’iyya.

Ko a baya-bayan nan dai an samu ƙorafe-ƙorafe daga ɓangaren wasu daga cikin ƴan ƴan takararkari kama daga na shugabancin ƙananan hukumomi zuwa kuma na kansila.

Wataƙila ma wannan ce tasa wasu daga cikin masu riƙe da muƙamai a gwamnatin jihar Kano suka fara ajiye muƙamansu irin su Abdullahi Tanka Galadanchi da ya ajiye muƙamin sa a baya-bayan nan, ko da dai yanzu haka zaben ƙananan hukumomin na ƙara tunkaro wa, wanda za’a gudanar a ranar 26 ga watan Oktoban 2024.

Manyan Labarai

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren gwamnatin Kano da wani Kwamishina

Published

on

Jam’iyyar NNPP ta jihar Kano ta bayyana dakatar da sakataren gwamnatin jihar Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da Kwamishinan Sufuri na jihar Kano Muhammad Diggwal, daga cikin jam’iyyar.

Shugaban jam’iyyar NNPP a Kano Dakta Hashim Sulaiman Dungurawa ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a cikin daren yau Litinin.

Hashim Dungurawa, ya ce dakatar da ƙusoshin gwamnatin jihar Kano su biyu ya biyo bayan zargin keta alfarmar jagoranci, da ta Jam’iyya, da kuma keta alfarmar gwamnati, a don haka ne suka ɗauki matakin ba tare da yin wasa ba akai.

“Jagorancin shugabancin jam’iyyar mu na ƙananan hukumomin da mutane biyun suka fito sun gabatar mana da ƙorafe-ƙorafe kan ƙusoshin gwamnatin biyu, akan zarge-zarge da ake musu ya sa muka ɗauki matakin dakatar da su, har sai mun gama bincike, “in ji Dungurawa”.

Sulaiman ya ƙara da cewar dakatar da Abdullahi Baffa Bichi da Muhammad Diggwal ta fara aiki ne daga ranar Litinin 14 ga watan Oktoban 2024, kamar yadda jam’iyyar ta samu ingantattun shawarwari akan zargin da ake musu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ku tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa na Ɗorayi bisa halin da suke ciki – Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam 

Published

on

Ƙungiyar wayar da kan jama’a da kare haƙƙin ɗan adam da tallafawa mabuƙata, ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, ta tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa da ke unguwar Ɗorayi, da dafaffen abinci, domin rage musu wata damuwa.

Ƙungiyar dai ta rabawa masu lalurar Ƙwaƙwalwar abincin ne da yammacin Asabar 12 ga watan Oktoban 2024, tare da ziyartar wata makarantar tsangaya da ke unguwar Ɗorayi, inda ɗalibai 1,000 suka rabauta da tallafin dafaffen abincin.

Da yake yiwa Dala FM Kano, ƙarin bayani daraktan ƙungiyar ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, Kwamared Auwal Usman, ya ce rahotannin da suka samu kan yadda mazauna Asibitin da kuma makarantun tsangayar ke fuskantar ƙalubalen abinci ya sa suka kai musu tallafin domin rage musu wani raɗaɗi.

 

Wasu daga cikin masu lalurar Ƙwaƙwalwar da suka fara samun sauƙi, sun nemi ɗaukin gwamnatin jihar Kano wajen magance ƙalubalen da suke fuskanta na rashin kyawun wuraren da suke kwana da sauran matsaloli, ko sa samu wani sauƙi.

Da yake nasa jawabin mai kula da Asibitin da ake kula da masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi a Kano, Munnir Ɗahiru Kurawa, ya miƙa godiyar sa ga tawagar ƙungiyar bisa kaɓakin alkhairin da ta saukewa masu taɓin hankalin.

Wannan dai na zuwa ne makwanni kaɗan da gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ziyarci Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi, har ma ya bada umarnin aje a gyara shi, sai dai kawo yanzu hakan bata samu ba kamar yadda wata majiya ta bayyana.

Continue Reading

Manyan Labarai

Mun biya wa mazauna gidan gyaran hali tara don rage musu raɗaɗi a Kano – Human Right

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Right Network, ta biya wa wasu mazauna gidan ajiya da gyaran hali na Goron da na yara da ke Kano, su 10 tara, waɗanda suka shaƙi iskar ƴanci.

Shugaban gudanarwar ƙungiyar na ƙasa Kwamared Tasi’u Idris Idris (Soja) ne ya bayyana wa manema labarai hakan jim kaɗan da fitowar su daga gidan gyaran halin lokacin da mutanen suka shaƙi iskar ƴanci a ranar Alhamis.

Tasi’u Idris ya ce sun ɗauki matakin biya wa mutanen tarar ne ciki har da Matasa domin su shaƙi iskar ƴanci kamar kowa, duba da halin matsin rayuwar da ake ciki yanzu a ƙasar nan.

Kasancewar guda daga cikin mambobin ƙungiyar ne na ƙaramar hukumar Kura mai suna Usman Yusuf Gun-Dutse, haɗin gwiwa da uwar ƙungiyar ta ƙasa ne suka biya tarar, a don haka ne muka zanta da shi, inda ya ce ya yi hakan ne domin taimaka wa mutanen.

Da yake nasa jawabin akan batun mai magana da yawun gidajen gyaran halin na jihar Kano SC Musbahu Lawan Ƙofar Nassarawa, ya ce abinda ƙungiyar ta yi abin jin daɗi ne bisa yadda aka rage cunkoson mutane a gidajen.

Majiyar tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewar, tuni dai mutanen suka koma cikin ƴan uwan su domin ci gaba da gudanar da harkokin su na yau da kullum.

Continue Reading

Trending