Connect with us

Manyan Labarai

Babu abinda zai sauya kan zaɓen ƙananan hukumomi a Kano- Hukumar Zaɓe

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano Kanseic, ta ce babu abinda zai sauya a zaɓen ƙananan hukumomin da za’a gudanar a ranar Asabar mai zuwa 26 ga watan Oktoban 2024.

Kwamishina mai kula da harkokin yaɗa labarai da al’amuran shari’a na hukumar zaɓen Lawan Badamasi ne ya bayyana hakan ta cikin shirin Barka da Hantsi na Freedom Radio da ya gudana a ranar Alhamis.

Ya kuma ce za kuma su yi amfani da jami’an tsaron cikin gida irin su Karota, da Ƴan Bijilante da sauransu, domin bayar da tsaro yayin zaɓen, biyo bayan umarnin da wata babbar kotun tarayta ta umarci jami’an tsaron ƴan sanda kan su ƙauracewa wurin zaɓen ƙananan hukumomin.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki biyu da babbar kotun tarayyar ta dakatar da shugabancin hukumar zaɓen ta Kano Kanseic, ko da dai hukumar ta ce babu fashi kan gudanar da zaɓen, wanda majalisar dokokin jihar itama ta ce babu fashi kan yin zaɓen.

Dala FM Kano, ta rawaito ko a ranar Laraba ma yayin da gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya bai wa mai martaba Sarkin Ƙaraye Alhaji Muhammad Muhammad Mahraz, sandar kama aiki, ya ce za’a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin a ranar Asabar kamar yadda aka tsara.

Manyan Labarai

Haihuwa a gida na janyo rasa rai – Dr. Hadiza Ashiru

Published

on

Ƙwararriyar likitar Yara da ke asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano Dakta Hadiza Ashiru, ta shawarci mata masu juna biyu cewar, da zarar sun fara jin alamun Naƙuda su rinƙa hanzarin zuwa Asibiti, domin a basu agajin gaggawa, don gujewa fuskantar matsala ga lafiyar su.

Dr. Hadiza Ashiru, ta bayyana hakan yayin zantawar ta da tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 14 ga watan Mayun 2025.

Ta ce abin takaici ne yadda mace mai juna biyu take shafe tsawon lokaci tana zuwa Awo, amma idan Haihuwa ta zo mata take ƙauracewa zuwa Asibiti, lamarin da ta ce idan haihuwar ta zo da kuskure ana iya rasa ran macen, ta sha wahala daga ƙarshe a tafi da ita Asibiti babu shiri.

“Duk da aikin mu na likitanci da muke yi a Asibiti, amma a haka mu ke shiga lungu da saƙo muna wayar da kan mata domin faɗakar da su illar cutar sankarar bakin mahaifa, wadda ke haifar da yawaitar mutuwar su a yayin haihuwa, “in ji Dr. Hadiza”.

Har ila yau, likitar ta kuma ce, idan matsala ta faru da macen ana shan wahala wajen shawo kan matsalar, a don haka mata masu juna biyu su rinƙa zuwa Asibiti, domin su Haihu a can, don su samu wani sauƙi.

Continue Reading

Manyan Labarai

Za ayi dokar da za ta tilastawa kamfanoni ɗaukar ma’aikata kashi 75 ƴan Kano – Gwamnati

Published

on

A ƙoƙarin ta na ƙara samarwa Matasa aikin yi, gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin yin dokar da za ta tilastawa kamfanoni masu zaman kansu ɗaukar kashi 75 cikin 100, na ma’aikata yan asalin jihar Kano.

Rahotanni sun bayyana cewa akan batun ne ma gwamnatin jihar Kano ta kafa wani kwamitin da zai rinƙa kula da ɗaukar ma’aikata bisa ƙa’ida a jihar.

A lokacin da yake ƙarin bayani yayin wani taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki ranar Laraba a Kano, shugaban kwamitin, Dakta Ibrahim Garba, ya ce za a miƙa daftarin dokar ga majalisar dokokin jihar da kuma gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, domin amincewa da dokar.

“Za’a ɗauki wannan mataki ne da nufin magance matsalar rashin aikin yi da kuma zaman kashe-wando tsakanin matasa a faɗin jihar Kano, “in ji shi”.

Kazalika, Garba ya bayyana cewa Gwamna Abba Yusuf, ya kafa kwamitin ne domin magance damuwar da ƴan jihar ke fuskanta dangane da yadda wasu kamfanoni masu zaman kansu suke ƙin ɗaukar ƴan asalin jihar aiki a kamfanonin su.

Continue Reading

Manyan Labarai

Hisba za ta fara kamen matan auren masu zaman Majalisa a Kano

Published

on

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta ce za ta fara kamen matan auren da suke zaman majalisa a cikin unguwanni, domin daƙile matsalar da ake fuskanta tsakanin ma’aurata.

Mataimakin babban kwamandan hukumar Hisbah na jihar Kano Dakta Mujahideen Aminudden Abubakar, shi ke ya bayyana hakan a zanatawar sa da gidan rediyon Dala FM Kano, a ranar Laraba.

Ya ce hukumar ta lura da yadda zaman majalisar da wasu daga cikin matan aure suke yi, ke haifar da gulmace-gulmace, da yawo a gari, da kuma ɓatawa wasu rayuwa ta hanyar koya musu neman Mata da sauran Laifuka.

“Za mu sanya ƙafar Wando ɗaya da dukkanin matan aure masu zaman majalisa a cikin unguwanni, bisa yadda hakan ya saɓawa doka; jami’an mu za su fara yawo a cikin daren kaya don ɗakile wannan matsalar”in ji shi”.

Dr. Mujahedden, ya kuma yi kira ga magidanta da su ƙara kula da shige da ficen matan su, don gujewa fuskantar matsala a zamantakewar auren su.

Continue Reading

Trending