Manta Sabo
Kotu ta umarci CBN da ya sakarwa ƙananan hukumomin Kano kuɗaɗen su.

Babbar kotun jaha karkashin jagorancin mai Shari’a Ibrahim Musa Ƙaraye, ta dakatar da babban bankin Najeriya CBN, da ofishin babban akanta na kasar nan daga yin jinkiri wajen biyan ƙananan hukumomin Kano kudadensu na arzikin kasa da gwamnatin tarayya ke bayarwa.
Cikin wata ƙara wadda shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomin Kano da mutane shida amadadin ƙungiyar suka shigar.
Waɗanda ake karar dai a gaban kotun sun hadar da babban akanta na kasar nan da kuma babban bankin Najeriya CBN, sai kuma wasu bankuna guda 7 da dukkanin ƙananan hukumomin Kano.
Masu ƙarar ta bakin lauyan su Barrister Bashir Yusuf Tudun Wuzurci, sun bayyana wa kotun cewar idan aka hana ƙananan hukumomin kudadensu hakan zai haifar da koma baya a jahar Kano kuma yin hakan ya saɓawa doka.
Kotun ta amince da dukkan roke-roken masu karar inda aka kùma ayyana cewar kodai babban bankin ƙasa CBN, ko babban akanta na kasar da ragowar waɗanda aka yi karar ko yan korensu cewar kada su yi jinkiri wajen biyan ƙananan hukumomin Kano kudadensu na arzikin kasa da ake rabawa kowace karamar hukuma.
Kotun ta kuma yi umarni da a aikewa waɗanda ake ƙara kwafin umarnin da ta bayar.
Wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya ruwaito cewar kotun ta sanya ranar 21 ga wannan watan dan sauraren kowanne ɓangaren.

Manta Sabo
Kotu ta ɗaure wani Matashi kan ji wa mahaifiyar sa rauni da Wuƙa a Kano

Wata kotun Majistret mai lamba 44 a Kano, ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Muhammad Alhaji Isah, ta hori wani matashi da ɗaurin shekara ɗaya ba tare da zaɓin tara ba.
Tunda fari dai matashin mai suna Muhammad Inuwa ɗan unguwa uku, Ƴan Sanda ne suka gurfanar da shi bisa zargin sa da ji wa mahaifiyarsa rauni da Wuka, wanda ya amsa laifinsa nan take.
Yayin zaman kotun ta tambaye shi ko yana da wani hanzari kafin hukunci, inda ya bayyana wa kotun cewar sharrin shaiɗan ne, kuma yana ta’ammali da miyagun Ƙwayoyi.
Kotun ta ayyana ɗaurin watanni 12 babu zaɓin tara a kan matashin, an kuma umarce shi da ya zama mutumin kirki, kamar yadda wakilin gidan rediyon Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Ismail ya ruwaito labarin.
Ko a yan kwanakin nan ma dai sai da hukumar hana sha da fataucin miyagun Ƙwayoyi NDLEA, suka bayyana cewar ta’ammali da miyagun Ƙwayoyi kan jawo wa mutum dana sani.

Manta Sabo
Zargin ɓata suna: Kotu ta bada Belin Ƴar TikTok Alpha Chales Borno

Kotun Majistret mai lamba 17 karkashin jagoranci mai Shari’a Huda Haruna Abdu, ta bayar da belin matashiyar yar Tiktok din nan Alpha Charles, wadda Ƴan Sanda suka gurfanar a gaban bisa zargin ta da laifin ɓata suna.
Ƙunshin zargin ya bayyana cewar Alpha Charles, ta ɓata sunan Sadiya Haruna ta dandalin sada zumunta.
Yayin da aka karanta mata tuhumar ta musanta, kuma lauyoyin da suke kare ta sun roki beli, Inda kotun ta sanya ta a hannun beli a bisa sharadin mutum biyu da za su tsaya mata,
Kazalika, sharuɗan Belin sun bayyana cewa, dole ne masu tsayawar na ɗaya ya zama ɗan uwanta na jini, ɗayan kuma ma’aikacin gwamnati mai mataki na 16, idan ta tsere masu karbar belin zasu ajiyewa kotun Naira dubu ɗari biyar.
Sai dai lauyan Alpha ya bayyana wa kotun cewar, Sadiya Haruna ta ɗauki hoto da bidoyon Alpha a harabar kotun ta kuma yaɗa a dandalin Facebook, tare da wasu maganganu da suke zargi na batanci ne.
A don haka kotun ta nemi mai ƙara Sadiya Haruna, sai dai an neme ta sama ko ƙasa ba a ganta ba, an kuma umarci lauyanta da ya gabatar da ita.
Wakilin Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, kotun ta sanya ranar 28 ga wannan watan Afrilun da ake ciki na shekarar 2025, don ci gaba da sauraron shari’ar.

Baba Suda
Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.
Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.
Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su