Connect with us

Manyan Labarai

Zargin Baɗala: Kotu ta wanke Auwalu Sankara da Taslim Baba Nabegu a Kano.

Published

on

Babbar kotun Shari’ar Muslunci mai zaman ta a kofar kudu ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Ibrahim Sarki Yola, ta sallami dakataccen kwamishina a jihar Jigawa, Auwalu Ɗanladi Sankara da Taslim Baba Nabegu.

Tun da farko kotun ce ta tura ofishin ƴan Sanda Shiyya ta ɗaya da ke jihar Kano, wato Zone 1, domin mukaddashin babban sifetan yansanda ya binciki zargin da ake wa Auwalu Danladi da Taslim Baba Nabegu, sakamakon korafin da wani mutum Mai suna Nasiru Buba ya yi, wanda ya zargi Auwalun da cewar suna yin mu’amalar da bata dace ba.

Cikin ƙunshin takaddar da muƙaddashin babban sifetan ƴansanda ya tura wa kotun ya bayyana cewar, hukumar Hisbah ta yi azarɓaɓi akan batun, kuma ya umarce su da su rinƙa yin aiki a bisa tsarin doka.

A zaman kotun na yau mai Shari’a Sarki Yola ya ayyana cewar babu tuhuma akan waɗanda ake zargin sakamakon yadda ƴan sanda suka gudanar da bincike, inda suka ce sun samu cewar maganar Jita-jita ce kuma Shari’a bata karɓar jita-jita.

Har ila yau, ma’aikatar Shari’a ta jahar Kano ta bayyana cewar babu tuhuma akan waɗanda ake zargin sakamakon rashin gamsassun hujjoji.

Mai Shari’a Ibrahim Sarki Yola ya ayyana cewar ya sallami Auwalu Danladi Sankara da Taslim Baba Nabegu nan take, kuma kotun ta umarci kowa ya zauna lafiya.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, da yake jawabi lauyan wanda ake ƙara Barrister Saddam Sulaiman, ya ce dama maganar siyasa ce ta shigo cikin al’amarin.

Manyan Labarai

Daba a Kano: Mun kama matasa 51 a cikin kwanaki uku – Ƴan Sanda

Published

on

A ƙoƙarin ta na magance harkokin faɗan Daba da fashin Waya, rundunar Ƴan Sandan jihar Kano, ta kama Matasa 51, cikin kwanaki uku a birnin jihar, tare da samun da muggan Makamai da kuma kayan maye.

A cikin sanarwar da mataimakin kakakin rundunar ƴan sandan jihar DSP Hussain Abdullahi, ya fitar a cikin daren Litinin, ta ce an kama matasan ne a ƙananan hukumomin ƙwaryar birnin Kano, irin su Tarauni, da Gwale, da Dala, Kano Municipal, a cikin unguwannin Zage, Ƙofar Mata, Kurna, da Rijiyar Lemo, Hotoro, da Sheka.

Rundunar ƴan sandan ta kuma ce ba za ta lamunci yadda wasu matasa ke amfani da makamai yayin kiɗan Gangi, lamarin da a wasu lokutan ake ɗaukar su a bidiyo, ko Hotuna riƙe da makamai ana yaɗawa a shafukan Tik-Tok, Facebook, X, da Instagram, da sauran su, abinda ke ƙarawa masu faɗan daban ƙwarin gwiwa akan lamarin.

Cikin sanarwar, Kwamishinan ƴan sandan jihar Kano Ibrahim Adamu Bakori, ya kuma buƙaci iyaye da su ƙara bibiyar al’amuran ƴaƴan su, tare da ɗaukar matakan da suka dace da zarar sun ga halayyar ƴaƴan nasu ta fara canzawa.

A cewar sanarwar, duk wanda ya ga faruwar wani abu da ka iya kawo matsalar tsaro zai iya kiran waɗannan lambobin wayar domin bada bayanan sirri, akan 08032600299, ko 08032600300, ko kuma 08032600301.

Rundunar ta kuma nuna jin daɗin ta bisa haɗin kan da take samu daga ɓangaren al’umma, a ƙoƙarin su na tabbatar da tsaro da zaman lafiya a faɗin jihar Kano.

Kwamishinan ƴan sandan na jihar Kano Ibrahim Bakori, ya kuma bada umarnin fara wasu ayyuka na ba sani ba sabo, amma fa sai an ɗauka da Hakuri, da ƴan daban, da kuma iyayen da suka bar Makami a Gidansu.

Tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewa, ko a ranar Asabar dai, sai da Kwamishian ƴan sandan Kano ta ƙaddamar da sabbin dabarun daƙile harkokin faɗan Daba da fashin Waya da Makami, da sauran ayyuka, a jihar, bayan ganawar sa da manyan jami’an tsaro.

Continue Reading

Manyan Labarai

Mun shirya ɗaukar mataki a kan ƴan siyasar da ke ɗaukar nauyin Ƴan Daba a Kano – Anti-Phone Snaching

Published

on

Rundunar Tsaro da ke yaki da fadan Daba da fashi da makamin Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye ta Anti-Phone Snaching, a jihar Kano, ta ce ta gano cewar yadda wasu daga cikin ‘Yan Siyasa ke daukar nauyin ‘Yan Daba na daga cikin daga cikin dalilan da ke kara ta’azzarar ayyukan ‘yan daban a sassan jihar.

Kwamandan rundunar a Kano Inuwa Salisu Sharada ne ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Litinin, ya ce yanzu haka sun fara bibiya tare da bincike akan irin matasan da suke damun jama’a da fadan Daba a sassan jihar Kano, don gano ‘Yan siyasar da ke da hannu akan lamarin tare da daukar mataki na gaba.

“Abin takaici ne yadda mafi yawancin masu fadan daban ake samun su kananan yara da ba su wuce shekaru 15 zuwa kasa ba, kuma duk da hakan duk wanda mu ka kama ba za mu saurara masa ba, a don haka ne ma mu ke kira ga iyaye da su tsawatar wa ya’yansu, in ji Inuwa”.

A cewar sa, idan suka kama masu harkar faɗan Daba, mafi yawancin su suna kama faɗin wasu daga cikin ƴan siyasa da suke ɗaukar nauyin su, kuma yanzu haka sun dukufa don gano bakin zaren tare da ɗaukar matakin da ya dace akan dukkan masu hannu kan lamarin.

Tuni dai kwamishinan ‘Yan sandan jihar Kano Ibrahim Adamu Bakori, ya kaddamar da sabbin dabarun magance harkokin Daba da fashin Waya da kuma shaye-shayen kayan maye a sassan jihar, bayan da ya gana da manyan jami’an ‘yan sandan a ranar Asabar din da ta gabata.

Continue Reading

Manyan Labarai

Kwamishinan Ƴan sandan Kano ya ƙaddamar da sabbin matakan daƙile Daba da Fashin Waya a jihar

Published

on

Rundunar Ƴan sandan jihar Kano ta sha alwashin kakkaɓe matsalar faɗab Daba, da fashin waya da makami, da Shaye-shayen kayan maye, da ke addabar jama’a a birnin jihar, don wanzar da zaman lafiya.

Kakakin rundunar ƴan Sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikewa manema labarai tashar Dala FM ta samu a ranar Lahadi 15 ga watan Yunin 2025.

Kiyawa, ya ce hakan na zuwa ne bayan da kwamishinan ƴan sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya ƙaddamar da sabbin matakan daƙile ayyukan ’yan daba da masu fashin waya da makami a birnin Kano da kewaye.

Sanarwar ta bayyana cewa kwamishinan ya gana da manyan jami’an rundunar ne a ranar Asabar 14 ga watan Yunin 2025, inda ya umarce su da su soma sumame a dukkan maɓoyar Ƴan Daba, tare da haɗin gwiwa da shugabannin al’umma domin ganin an cafko duk masu hannu a tashe-tashen hankula a faɗin jihar.

“A umarnin da kwamishinan ya bayar, ya umarci dukkanin Baturen Ƴan Sanda wato DPO’s, da shugabannin shiyya na Ƴan Sanda, da sauran dakarun Ƴan sanda, da su nemi haɗin kai da al’umma, tare da ƙara faɗaɗa sintiri don magance matsalolin Daba, da fashin Waya a Kano, in ji Kiyawa”

Har ila yau, rundunar ƴan sandan ta kuma buƙaci haɗin kan jama’a da su rika bayar da bayanan sirri a kan yan daban, ta hanyar kiran waɗannan lambobin wayar 08032419752, ko 08123821575, 09029292926.

Continue Reading

Trending