Connect with us

Manta Sabo

Kotu ta hana duk wata kafar yada labarai yin labarin da ya shafi Auwalu Danladi Sankara da Taslim Baba Nabegu.

Published

on

Babbar kotun jaha mai lamba 4 karkashin jagorancin mai Shari’a Usman Na Abba ta yi hani ga duk wasu Jami’an Ƴan sanda ko na duk wata hukuma ta daban daga gayyata ko tsangwama, ko kuma bincike ko kamawa, ta kowace siga ga kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa Auwalu Ɗanladi Sankara.

Wannan dai na zuwa ne bayan da kotu ta wanke Auwalu Sankara daga zargin mu’amala ko alaƙa da juna tsakanin mai ƙara da Taslim Baba Nabegu har zuwa lokacin sauraran ƙarar.

Kotun ta kuma amince da rokon da wani lauya mai suna Barrister I.C Ekpinovi ya yi amadadin mai kara Auwalu Danladi Sankara wanda ya yi karar Nasiru Buba.

Mai karar ta bakin lauyansa ya bayyana wa kotun rokonsa inda ya roki kotun da ta dakatar da wanda ake kara ko dai shi da kansa ko kuma ƴan korensa daga ci gaba da yaɗa wata magana wadda wata babbar kotun Shari’ar Muslunci da ke Kano ta rufe.

Mai Shari’a Usman Na Abba ya ayyana cewar ko dai wanda aka yi kara ko yan korensa ko kuma wasu wakilansa, da a dai na yaɗa waccan magana har zuwa lokacin da kotun za ta saurari kowanne ɓangare.

Kotun ta ayyana cewar ta yi hani ga duk wata kafa ta yada labarai ko dai Rediyo ko Talabijin, ko shafukan sada zumunta da kafar Intanet da duk wata kafa wadda take iya sadar da labarai, daga yaɗa labaran da suka shafi Auwalu Ɗanladi Sankara da Taslim Baba Nabegu.

A ranar Talata ne dai gwamnan jihar Jigawa Mallam Umar Namadi ya bayyana mayar da Auwalu Ɗanladi Sankara muƙamin sa na Kwamishinan ayyuka na musamman a jihar, bayan da kotu ta wanke shi daga zargin da hukumar Hisbah ta Kano, ta yi masa kan zargin baɗala da wata matar aure.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa kotun ta kuma sanya ranar 28 ga wannan watan na Nuwamba dan sauraron kowane ɓangare akan shari’ar.

Manta Sabo

Zargin Kisa: Kotu ta aike da Matashi gidan Yari a Kano

Published

on

Kotun Majistret mai lamba 16 ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Alkasim Nasib Ɗan Fillo, ta aike da wani matashi gidan gyaran hali bisa zargin sa da laifin kisan kai.

Tunda fari, Ƴan Sanda ne suka gurfanar da matashin suna zargin sa da laifin haɗa baki da fashi da makami, da kuma laifin kisan kai.

Ƙunshin zargin ya bayyana cewar, a ranar 5 ga wannan watan na Mayun 2025, ne matashin mai suna Aliyu Umar, suka haɗa baki da wasu matasa waɗanda a yanzu sun tsere, inda suka shiga gidan wani mutum mai suna Muhammad Shehu.

An yi zargin cewa bayan sun shiga gidan mutumin sun yi amfani da muggan makamai suka yi masa fashin wayar Salula, daga ƙarshe an zargi cewa sun soka masa Wuƙa a Maƙogoro har rai ya yi halinsa.

Yayin da aka karanta wa matashin ƙunshin zargin ya bayyana cewar ya fahimta, daga nan ne kotun ta bayyana cewar bata da hurumin yin shari’ar kisan kai, a don haka za ta jira shawarar lauyoyin gwamnati.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewar, an sanya ranar 26 ga watan gobe don a kara gabatar da matashin a gaban kotu.

Continue Reading

Manta Sabo

Kotu ta tura Amarya da Angon ta gidan Yari a Kano

Published

on

Babbar kotun shari’ar Musulunci da ke zamanta a Post Office, a Kano, ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Munzali Tanko Soron Ɗinki, ta aike wata mata da wani mutum gidan gyaran hali zuwa Mako ɗaya, bisa zargin su da Aure akan Aure.

 

Tunda fari wani magidanci ne ya maka matarsa da wani mutum da ya same shi a ɗakinsa a gaban kotu, ko da dai matar ta ce wai wanda mijin nata ya gani shima mijinta ne.

Lamarin dai ya faru ne a unguwar Tudun Murtala, inda mai ƙarar ya zo gidan matarsa kasancewar yanada wasu matan, sai ya sami wani mutum a kwance akan gadan matar, inda nan take ya tambaye shi waye shi? sai matar ta ce ɗan uwanta ne, hakan ya sa ya gayyato Maƙota su ka zo domin su shaida faruwar lamarin.

Daga bisani ne kuma ya garzaya babbar kotun shari’ar Musulunci da ke Post Office a jihar Kano, ƙarƙashin mai shari’a Munzali Tanko Soron Ɗinki, inda ya yi ƙarar sabon mijin da matar.

Mutumin ya faɗawa kotun cewar shekararsu shida ke nan da Aure a tsakanin su, amma kwatsam sai ya sami wani a ɗakinta, kuma ya ce kwana biyu tsakani ya yi mu’amular Aure da ita.

Sai dai sabon mijin ya ce matar ta faɗa masa bata da Aure, hakan ya sa ya tura wakilansa aka biya dubu ɗari a matsayin sadaki har aka ɗaura musu auren.

 

Ko da Kotu ta wai-wayi matar ta ce ai babu aurensa a kanta bayan samun magana mai karo da juna, a nan ne mai Shari’a ya tambayi asalin waliyinta, inda shi kuma ya ce bai san ta yi wani auren ba.

Hakan yasa kotu ta bukaci ta rantse akan ya saketa sai dai ta ce Eh, aka tambayeta ko za ta rantse ta ce A’a, akace shi tsohon mijin zai rantse ya ce zai rantse, nan take ta ce ba za ta bari ya rantse ba.

Daga bisani kotun ta buƙaci a turasu wajan yan sanda sannan matar ta ce za ta faɗi gaskiya.

 

Matar ta faɗawa kotun cewar tabbas ta yi aure akan Aure, a don haka take neman afuwa, a nan ne mai Shari’a ya aike da matar da sabon mijin gidan gyaran hali har zuwa sati daya domin yi mata hukunci, kamar yadda wakilinmu Aminu Abdu Baka Noma ya ruwaito.

Continue Reading

Manta Sabo

Kotu ta yi umarnin a kamo wani Dagaci a Kano

Published

on

Babbar kotun Shari’ar Muslunci da ke zaman ta a Rijiyar Lemo a nan Kano, ta yi umarnin yansanda su kamo mata dagacin garin Iya malam Lawan Ibrahim.

Tun da farko wani mutum ne mai suna Nura Musa Inuwa mazaunin Katsinawa, ya shigar da ƙara yana da’awar cewa ya sayi gona a hannun dagacin amma daga baya ya samu cewar dagacin ya sayar wa da wani mutum daban gonar.

A zaman dai, kotun ta yi umarnin a kamo mata dagacin a karkashin Shari’a mai lamba Cv/373/2024.

 

Wakilin Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Ismail, ya tuntuɓi dagacin ta wayar Salula, amma bai samu damar ɗagawa ba, ya kuma aike masa gajeren saƙo amma har zuwa lọkacin hada wannan labarin ba mu ji daga gare shi ba.

Continue Reading

Trending