Connect with us

Manyan Labarai

An yi jana’izar Shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano Ahmadu Haruna Zago

Published

on

Ɗaruruwan mutane ne suka halarci sallar jana’izar shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano Alhaji Ahmadu Haruna zago, wanda aka gudanar a kofar kudu a fadar mai martaba sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu.

Babban kwamandan hukumar Hisbah na jihar Kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, shine ya jagorancin sallar jana’izar a tsakar ranar Alhamis ɗin nan.

Daga cikin manyan manyan mutane da Suka hallarci sallar jana’izar marigayin Alhaji Ahmadu Haruna zago, akwai gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da tsohon kwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwakwanso, da mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, da sauran manyan mutane ciki har da masu riki da mukaman gwamiti.

Da safiyar Alhamis ɗin nan ne dai marigayi Ahmadu Zago, mai shekaru 74 ya rasu, a Asibitin Aminu Kano, bayan fama da rashin lafiya, kafin rasuwar sa yana da mata huɗu da ƴaƴa 37, da jikoki da dama.

Mai martaba sarkin kano Khalifa Muhammadu Sunusi na yayi addu’ar fatan Allah ya jikan marigayin ya kuma baiwa iyalansa da al’ummar jihar Kano jure rashin.

Tuni dai gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya miƙa saƙon ta’aziyyar sa ga al’ummar jihar da kuma iyalan marigayi Ahmadu Haruna Zago, tare da fatan Allah ya gafarta masa.

Baba Suda

Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.

 

Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.

 

Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Continue Reading

Manyan Labarai

Da Ɗumi-Ɗumi! Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakin sa da ƴan majalisar jihar na watanni 6.

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.

Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani taƙaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.

Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin ƴan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan, tare da sanya dokar ta ɓaci a jihar.

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya daɗe da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saƙa tsakanin sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Continue Reading

Manyan Labarai

Isra’ila ta kashe sama da mutane 200 bayan karya yarjejeniyar tsagaita Wuta a Gaza

Published

on

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, tare da ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasdinawa.

Jaridar TRT Hausa ta ruwaito cewa, aƙalla Isra’ila ta kashe fiye da mutum 200 tare da jikkata ɗaruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti, kamar yadda majiyoyin wani asibiti a yankin Gaza suka bayyana.

Continue Reading

Trending